< Ayuba 42 >
1 Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Da svarede Job Herren og sagde:
2 “Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
Jeg ved, at du formaar alting, og at ingen Tanke er dig forment.
3 Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
„Hvo er den, som fordunkler Guds Raad uden Forstand‟? — Saa har jeg udtalt mig om det, som jeg ikke forstod, om de Ting, som vare mig for underlige, hvilke jeg ikke kendte.
4 “Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
Hør dog, og jeg vil tale; jeg vil spørge dig, og undervis du mig!
5 Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
Jeg havde hørt om dig af Rygte, men nu har mit Øje set dig.
6 Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
Derfor forkaster jeg, hvad jeg har sagt, og angrer i Støv og Aske.
7 Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
Og det skete, efter at Herren havde talt disse Ord til Job, da sagde Herren til Elifas, Themaniten: Min Vrede er optændt imod dig og imod dine to Venner; thi I have ikke talt ret om mig, saaledes som min Tjener Job.
8 Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
Saa tager eder nu syv Tyre og syv Vædre, og gaar til min Tjener Job, og ofrer Brændoffer for eder, og Job, min Tjener, skal bede for eder; ikkun hans Person vil jeg anse, at jeg ikke skal lade eders Daarlighed gaa ud over eder; thi I have ikke talt ret om mig, saaledes som min Tjener Job.
9 Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
Saa gik Elifas Themaniten og Bildad Sukiten og Zofar Naamathiten, og de gjorde, ligesom Herren havde sagt til dem; og Herren ansaa Jobs Person.
10 Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
Og Herren vendte Jobs Fangenskab, der han havde bedet for sine Venner; og Herren forøgede alt det, Job havde haft, til det dobbelte.
11 Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
Og alle hans Brødre og alle hans Søstre og alle, som kendte ham tilforn, kom til ham og aade Brød med ham i hans Hus og viste ham Deltagelse og trøstede ham over alt det onde, som Herren havde ladet komme over ham; og de gave ham hver en Penning og hver et Smykke af Guld.
12 Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
Og Herren velsignede Jobs sidste Levetid fremfor den første; og han fik fjorten Tusinde Faar og seks Tusinde Kameler og tusinde Par Øksne og tusinde Aseninder.
13 Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
Og han fik syv Sønner og tre Døtre.
14 ’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
Og han kaldte den førstes Navn Jemima og den andens Navn Kezia og den tredjes Navn Keren-Happuk.
15 Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
Og der blev ikke fundet saa dejlige Kvinder som Jobs Døtre i hele Landet, og deres Fader gav dem Arv iblandt deres Brødre.
16 Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
Og Job levede derefter hundrede og fyrretyve Aar og saa sine Børn og sine Børnebørn i fjerde Slægt.
17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.
Og Job døde, gammel og mæt af Dage.