< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
Bwana akamwambia Ayubu:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
“Je, mwenye kushindana na Mwenyezi aweza kumsahihisha? Mwenye kumlaumu Mungu na ajibu.”
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Ndipo Ayubu akamjibu Bwana:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
“Mimi sistahili kabisa: ninawezaje kukujibu wewe? Nauweka mkono wangu juu ya kinywa changu.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
Nimesema mara moja, lakini sina jibu; naam, nimesema mara mbili, lakini sitasema tena.”
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Ndipo Bwana akasema na Ayubu kutoka upepo wa kisulisuli:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
“Jikaze kama mwanaume; nitakuuliza maswali, nawe yakupasa unijibu.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
“Je, utabatilisha hukumu yangu? Utanilaumu mimi ili kujihesabia haki mwenyewe?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Je, una mkono kama wa Mungu, nawe waweza kutoa sauti ya ngurumo kama yake?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Basi jivike mwenyewe utukufu na fahari, nawe uvae heshima na enzi.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Fungulia ukali wa ghadhabu yako, mtafute kila mwenye kiburi umshushe,
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
mwangalie kila mtu mwenye kiburi na umnyenyekeze, waponde waovu mahali wasimamapo.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Wazike wote mavumbini pamoja; wafunge nyuso zao kaburini.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Ndipo mimi mwenyewe nitakukubalia kuwa mkono wako mwenyewe wa kuume unaweza kukuokoa.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
“Mwangalie mnyama aitwaye Behemothi, niliyemuumba kama nilivyokuumba wewe, anayekula majani kama ngʼombe.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Tazama basi nguvu alizo nazo kwenye viuno vyake, uwezo alio nao kwenye misuli ya tumbo lake!
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Mkia wake hutikisika kama mwerezi; mishipa ya mapaja yake imesukwa pamoja.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Mifupa yake ni bomba za shaba, maungo yake ni kama fito za chuma.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Yeye ni wa kwanza miongoni mwa kazi za Mungu, lakini Muumba wake anaweza kumsogelea kwa upanga wake.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Vilima humletea yeye mazao yake, nao wanyama wote wa porini hucheza karibu naye.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Hulala chini ya mimea ya yungiyungi, katika maficho ya matete kwenye matope.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Hiyo mimea ya yungiyungi humficha kwenye vivuli vyake; miti mirefu karibu na kijito humzunguka.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Wakati mto ufurikapo, yeye hapati mshtuko wa hofu; yeye yu salama, hata kama Yordani ingefurika hadi kwenye kinywa chake.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Je, mtu yeyote anaweza kumkamata yeye akiwa macho, au kumnasa kwa mtego na kutoboa pua yake?

< Ayuba 40 >