< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
Et adiecit Dominus, et locutus est ad Iob:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Numquid qui contendit cum Deo, tam facile conquiescit? utique qui arguit Deum, debet respondere ei.
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Respondens autem Iob Domino, dixit:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Qui leviter locutus sum, respondere quid possum? manum meam ponam super os meum.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
Unum locutus sum, quod utinam non dixissem: et alterum, quibus ultra non addam.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Respondens autem Dominus Iob de turbine, dixit:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Accinge sicut vir lumbos tuos: interrogabo te: et indica mihi.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Numquid irritum facies iudicium meum: et condemnabis me, ut te iustificeris?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Et si habes brachium sicut Deus, et si voce simili tonas?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Circumda tibi decorem, et in sublime erigere, et esto gloriosus, et speciosis induere vestibus.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Disperge superbos in furore tuo, et respiciens omnem arrogantem humilia.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Respice cunctos superbos, et confunde eos, et contere impios in loco suo.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Absconde eos in pulvere simul, et facies eorum demerge in foveam:
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Et ego confitebor quod salvare te possit dextera tua.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Ecce, Behemoth, quem feci tecum, fœnum quasi bos comedet:
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Fortitudo eius in lumbis eius, et virtus illius in umbilico ventris eius.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Stringit caudam suam quasi cedrum, nervi testiculorum eius perplexi sunt.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Ossa eius velut fistulæ æris, cartilago illius quasi laminæ ferreæ.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Ipse est principium viarum Dei, qui fecit eum, applicabit gladium eius.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Huic montes herbas ferunt: omnes bestiæ agri ludent ibi.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Sub umbra dormit in secreto calami, et in locis humentibus.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Protegunt umbræ umbram eius, circumdabunt eum salices torrentis.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Ecce, absorbebit fluvium, et non mirabitur: et habet fiduciam quod influat Iordanis in os eius.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
In oculis eius quasi hamo capiet eum, et in sudibus perforabit nares eius.

< Ayuba 40 >