< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
L’Eterno continuò a rispondere a Giobbe e disse:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
“Il censore dell’Onnipotente vuole ancora contendere con lui? Colui che censura Iddio ha egli una risposta a tutto questo?”
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Allora Giobbe rispose all’Eterno e disse:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
“Ecco, io son troppo meschino; che ti risponderei? Io mi metto la mano sulla bocca.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
Ho parlato una volta, ma non riprenderò la parola, due volte… ma non lo farò più”.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
L’Eterno allora rispose a Giobbe dal seno della tempesta, e disse:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
“Orsù, cingiti i lombi come un prode; ti farò delle domande e tu insegnami!
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Vuoi tu proprio annullare il mio giudizio? condannar me per giustificar te stesso?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Hai tu un braccio pari a quello di Dio? o una voce che tuoni come la sua?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Su via, adornati di maestà, di grandezza, rivestiti di splendore, di magnificenza!
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Da’ libero corso ai furori dell’ira tua; mira tutti i superbi e abbassali!
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Mira tutti i superbi e umiliali! e schiaccia gli empi dovunque stanno!
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Seppelliscili tutti assieme nella polvere, copri di bende la lor faccia nel buio della tomba!
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Allora, anch’io ti loderò, perché la tua destra t’avrà dato la vittoria.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Guarda l’ippopotamo che ho fatto al par di te; esso mangia l’erba come il bove.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Ecco la sua forza è nei suoi lombi, e il vigor suo nei muscoli del ventre.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Stende rigida come un cedro la coda; i nervi delle sue cosce sono intrecciati insieme.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Le sue ossa sono tubi di rame; le sue membra, sbarre di ferro.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Esso è il capolavoro di Dio; colui che lo fece l’ha fornito di falce,
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
perché i monti gli producon la pastura; e là tutte le bestie de’ campi gli scherzano intorno.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Si giace sotto i loti, nel folto de’ canneti, in mezzo alle paludi.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
I loti lo copron dell’ombra loro, i salci del torrente lo circondano.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Straripi pure il fiume, ei non trema; rimane calmo, anche se avesse un Giordano alla gola.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Potrebbe alcuno impadronirsene assalendolo di fronte? o prenderlo colle reti per forargli il naso?

< Ayuba 40 >