< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
Et l’Éternel répondit à Job et dit:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Celui qui conteste avec le Tout-puissant l’instruira-t-il? Celui qui reprend Dieu, qu’il réponde à cela!
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Et Job répondit à l’Éternel et dit:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Voici, je suis une créature de rien, que te répliquerai-je? Je mettrai ma main sur ma bouche.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
J’ai parlé une fois, et je ne répondrai plus; et deux fois, et je n’ajouterai rien.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Et l’Éternel répondit à Job du milieu du tourbillon et dit:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Ceins tes reins comme un homme; je t’interrogerai, et tu m’instruiras!
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Veux-tu donc anéantir mon jugement? Me démontreras-tu inique afin de te justifier?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
As-tu un bras comme Dieu, et tonneras-tu de ta voix comme lui?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Pare-toi, je te prie, de grandeur et de magnificence; revêts-toi de majesté et de gloire!
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Répands les fureurs de ta colère, et regarde tout ce qui s’élève et abaisse-le;
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Regarde tout ce qui s’élève [et] humilie-le, et écrase sur place les méchants;
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Cache-les ensemble dans la poussière, lie leurs faces dans un lieu caché:
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Alors moi aussi je te célébrerai, parce que ta droite te sauve!
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Vois le béhémoth, que j’ai fait avec toi: il mange l’herbe comme le bœuf.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Regarde donc: sa force est dans ses reins, et sa puissance dans les muscles de son ventre.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Il courbe sa queue comme un cèdre; les nerfs de sa cuisse sont entrelacés;
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Ses os sont des tubes d’airain, ses membres sont des barres de fer!
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Il est la première des voies de Dieu: celui qui l’a fait lui a fourni son épée.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Car les montagnes lui apportent [sa] pâture, là où se jouent toutes les bêtes des champs.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Il se couche sous les lotus dans une retraite de roseaux et de marécages;
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Les lotus le couvrent de leur ombre, les saules de la rivière l’environnent.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Voici, que le fleuve déborde avec violence, il ne se précipite pas; il est plein d’assurance si un Jourdain se jette contre sa gueule.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Le prendra-t-on en face? Lui percera-t-on le nez dans une trappe?

< Ayuba 40 >