< Ayuba 40 >
1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
Yahweh s’adressant à Job, dit:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Le censeur du Tout-Puissant veut-il encore plaider contre lui? Celui qui dispute avec Dieu peut-il répondre?
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Job répondit à Yahweh, en disant:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Chétif que je suis, que te répondrai-je? Je mets la main sur ma bouche.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
J’ai parlé une fois, je ne répliquerai pas; deux fois, je n’ajouterai rien.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Yahweh parla encore à Job du sein de la tempête et dit:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Ceins tes reins, comme un homme; Je vais t’interroger, et tu m’instruiras.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Veux-tu donc anéantir ma justice, me condamner afin d’avoir droit?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
As-tu un bras comme celui de Dieu, et tonnes-tu de la voix comme lui?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Pare-toi de grandeur et de magnificence, revêts-toi de gloire et de majesté;
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
épanche les flots de ta colère, d’un regard abaisse tout superbe.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
D’un regard fais plier tout superbe, écrase sur place les méchants;
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
cache-les tous ensemble dans la poussière, enferme leur visage dans les ténèbres.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Alors, moi aussi, je te rendrai l’hommage, que ta droite peut te sauver.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Vois Béhémoth, que j’ai créé comme toi: il se nourrit d’herbe, comme le bœuf.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Vois donc, sa force est dans ses reins, et sa vigueur dans les muscles de ses flancs!
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Il dresse sa queue comme un cèdre; les nerfs de ses cuisses forment un solide faisceau.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Ses os sont des tubes d’airain, ses côtes sont des barres de fer.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
C’est le chef-d’œuvre de Dieu; son Créateur l’a pourvu d’un glaive.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Les montagnes produisent pour lui du fourrage, autour de lui se jouent toutes les bêtes des champs.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Il se couche sous les lotus, dans le secret des roseaux et des marécages.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Les lotus le couvrent de leur ombre, les saules du torrent l’environnent.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Que le fleuve déborde, il ne craint pas; il serait calme, si le Jourdain montait à sa gueule.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Est-ce en face qu’on pourra le saisir, avec des filets, et lui percer les narines?