< Ayuba 40 >
1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
And Yahweh responded to Job, and said: —
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Shall a reprover contend, with the Almighty? He that disputeth with GOD, let him answer it!
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Then Job responded to Yahweh, and said: —
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Lo! I am of no account, what shall I reply to thee? My hand, have I laid on my mouth:
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
Once, have I spoken, but I will not proceed, yea twice, but I will not add.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
So then Yahweh responded to Job, out of a storm, and said: —
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Gird, I pray thee—as a strong man—thy loins, I will ask thee, and inform thou me.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Wilt thou even frustrate my justice? Wilt thou condemn me, that thou mayest appear right?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
But if, an arm like GOD, thou hast, and, with a voice like his, thou canst thunder,
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Deck thyself, I pray thee, with majesty and grandeur, Yea, with dignity and splendour, thou shalt clothe thyself;
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Pour out thy transports of anger, and look on every one who is high, and lay him low;
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Look on every one who is high, and humble him, yea tread down the lawless, on the spot:
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Hide them in the dust all together, Their faces, bind thou in darkness;
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
And, even I myself, will praise thee, in that thine own right hand can bring thee salvation.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Behold, I pray thee, the Hippopotamus, which I made with thee, Grass—like the ox, he eateth;
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Behold, I pray thee, his strength in his loins, and his force, in the muscles of his belly;
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
He bendeth down his tail like a cedar, the sinews of his thighs, are twisted together;
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
His bones, are barrels of bronze, his frame, is like hammered bars of iron:
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
He, is the beginning of the ways of GOD, Let his maker, present him his sword:
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Surely the mountains bring, produce, to him, where, all the wild beasts of the field, do play;
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Under the lotus-trees, he lieth down, in a covert of reed and swamp;
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
The lotus-trees cover him with their shade, the willows of the torrent-bed compass him about;
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Lo! the river becometh insolent—he is not alarmed! He is confident, though a Jordan burst forth to his mouth:
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Before his eyes, shall he be caught? With a hook, can one pierce his nose?