< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
And the Lord went on, and said to Job:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Shall he that contendeth with God be so easily silenced? surely he that reproveth God, ought to answer him.
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Then Job answered the Lord, and said:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
What can I answer, who hath spoken inconsiderately? I will lay my hand upon my mouth.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
One thing I have spoken, which I wish I had not said: and another, to which I will add no more.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
And the Lord answering Job out of the whirlwind, said:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Gird up thy loins like a man: I will ask thee, and do thou tell me.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Wilt thou make void my judgment: and condemn me, that thou mayst be justified?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
And hast thou an arm like God, and canst thou thunder with a voice like him?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Clothe thyself with beauty, and set thyself up on high and be glorious, and put on goodly garments.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Scatter the proud in thy indignation, and behold every arrogant man, and humble him.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Look on all that are proud, and confound them, and crush the wicked in their place.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Hide them in the dust together, and plunge their faces into the pit.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Then I will confess that thy right hand is able to save thee.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Behold behemoth whom I made with thee, he eateth grass like an ox.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
His strength is in his loins, and his force in the navel of his belly.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
He setteth up his tail like a cedar, the sinews of his testicles are wrapped together.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
His bones are like pipes of brass, his gristle like plates of iron.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
He is the beginning of the ways of God, who made him, he will apply his sword.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
To him the mountains bring forth grass: there all the beasts of the field shall play.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
He sleepeth under the shadow, in the covert of the reed, and in moist places.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
The shades cover his shadow, the willows of the brook shall compass him about.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Behold, he will drink up a river, and not wonder: and he trusteth that the Jordan may run into his mouth.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
In his eyes as with a hook he shall take him, and bore through his nostrils with stakes.

< Ayuba 40 >