< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
И отвечал Елифаз Феманитянин и сказал:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
если попытаемся мы сказать к тебе слово, - не тяжело ли будет тебе? Впрочем кто может возбранить слову!
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Вот, ты наставлял многих и опустившиеся руки поддерживал,
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
падающего восставляли слова твои, и гнущиеся колени ты укреплял.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
А теперь дошло до тебя, и ты изнемог; коснулось тебя, и ты упал духом.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Богобоязненность твоя не должна ли быть твоею надеждою, и непорочность путей твоих - упованием твоим?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Вспомни же, погибал ли кто невинный, и где праведные бывали искореняемы?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Как я видал, то оравшие нечестие и сеявшие зло пожинают его;
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
от дуновения Божия погибают и от духа гнева Его исчезают.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Рев льва и голос рыкающего умолкает, и зубы скимнов сокрушаются;
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
могучий лев погибает без добычи, и дети львицы рассеиваются.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
И вот, ко мне тайно принеслось слово, и ухо мое приняло нечто от него.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Среди размышлений о ночных видениях, когда сон находит на людей,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
объял меня ужас и трепет и потряс все кости мои.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
И дух прошел надо мною; дыбом стали волосы на мне.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Он стал, - но я не распознал вида его, - только облик был пред глазами моими; тихое веяние, - и я слышу голос:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
человек праведнее ли Бога? и муж чище ли Творца своего?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Вот, Он и слугам Своим не доверяет и в Ангелах Своих усматривает недостатки:
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
тем более - в обитающих в храминах из брения, которых основание прах, которые истребляются скорее моли.
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Между утром и вечером они распадаются; не увидишь, как они вовсе исчезнут.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Не погибают ли с ними и достоинства их? Они умирают, не достигнув мудрости.

< Ayuba 4 >