< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Respondens autem Eliphaz Themanites, dixit:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
Si cœperimus loqui tibi, forsitan moleste accipies; sed conceptum sermonem tenere quis poterit?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Ecce docuisti multos, et manus lassas roborasti;
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
vacillantes confirmaverunt sermones tui, et genua trementia confortasti.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Nunc autem venit super te plaga, et defecisti; tetigit te, et conturbatus es.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Ubi est timor tuus, fortitudo tua, patientia tua, et perfectio viarum tuarum?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Recordare, obsecro te, quis umquam innocens periit? aut quando recti deleti sunt?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Quin potius vidi eos qui operantur iniquitatem, et seminant dolores, et metunt eos,
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
flante Deo perisse, et spiritu iræ ejus esse consumptos.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Rugitus leonis, et vox leænæ, et dentes catulorum leonum contriti sunt.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
Tigris periit, eo quod non haberet prædam, et catuli leonis dissipati sunt.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Porro ad me dictum est verbum absconditum, et quasi furtive suscepit auris mea venas susurri ejus.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
In horrore visionis nocturnæ, quando solet sopor occupare homines,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
pavor tenuit me, et tremor, et omnia ossa mea perterrita sunt;
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
et cum spiritus, me præsente, transiret, inhorruerunt pili carnis meæ.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Stetit quidam, cujus non agnoscebam vultum, imago coram oculis meis, et vocem quasi auræ lenis audivi.
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
Numquid homo, Dei comparatione, justificabitur? aut factore suo purior erit vir?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Ecce qui serviunt ei, non sunt stabiles, et in angelis suis reperit pravitatem;
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
quanto magis hi qui habitant domos luteas, qui terrenum habent fundamentum, consumentur velut a tinea?
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
De mane usque ad vesperam succidentur; et quia nullus intelligit, in æternum peribunt.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Qui autem reliqui fuerint, auferentur ex eis; morientur, et non in sapientia.

< Ayuba 4 >