< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
데만 사람 엘리바스가 대답하여 가로되
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
누가 네게 말하면 네가 염증이 나겠느냐 날지라도 누가 참고 말하지 아니하겠느냐
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
전에 네가 여러 사람을 교훈하였고 손이 늘어진 자면 강하게 하였고
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
넘어져 가는 자를 말로 붙들어 주었고 무릎이 약한 자를 강하게 하였거늘
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
이제 이 일이 네게 임하매 네가 답답하여 하고 이 일이 네게 당하매 네가 놀라는구나
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
네 의뢰가 경외함에 있지 아니하냐 네 소망이 네 행위를 완전히 함에 있지 아니하냐
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
생각하여 보라 죄없이 망한 자가 누구인가 정직한 자의 끊어짐이 어디 있는가
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
내가 보건대 악을 밭갈고 독을 뿌리는 자는 그대로 거두나니
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
다 하나님의 입기운에 멸망하고 그 콧김에 사라지느니라
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
사자의 우는 소리와 사나운 사자의 목소리가 그치고 젊은 사자의 이가 부러지며
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
늙은 사자는 움킨 것이 없어 죽고 암사자의 새끼는 흩어지느니라
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
무슨 말씀이 내게 가만히 임하고 그 가는 소리가 내 귀에 들렸었나니
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
곧 사람이 깊이 잠들 때쯤 하여서니라 내가 그 밤의 이상으로 하여 생각이 번거로울 때에
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
두려움과 떨림이 내게 이르러서 모든 골절이 흔들렸었느니라
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
그 때에 영이 내 앞으로 지나매 내 몸에 털이 주뼛하였었느니라
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
그 영이 서는데 그 형상을 분변치는 못하여도 오직 한 형상이 내 눈 앞에 있었느니라 그 때 내가 종용한 중에 목소리를 들으니 이르기를
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
인생이 어찌 하나님보다 의롭겠느냐 사람이 어찌 그 창조하신 이보다 성결하겠느냐
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
하나님은 그 종이라도 오히려 믿지 아니하시며 그 사자라도 미련하다 하시나니
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
하물며 흙 집에 살며 티끌로 터를 삼고 하루살이에게라도 눌려 죽을 자이겠느냐
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
조석 사이에 멸한 바 되며 영원히 망하되 생각하는 자가 없으리라
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
장막 줄을 그들에게서 뽑지 아니하겠느냐 그들이 죽나니 지혜가 없느니라

< Ayuba 4 >