< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
時にテマン人エリパズ答へて曰く
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
人もし汝にむかひて言詞を出さば汝これを厭ふや 然ながら誰か言で忍ぶことを得んや
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
さきに汝は衆多の人を誨へ諭せり 手の埀たる者をばこれを強くし
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
つまづく者をば言をもて扶けおこし 膝の弱りたる者を強くせり
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
然るに今この事汝に臨めば汝悶え この事なんぢに加はれば汝おぢまどふ
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
汝は神を畏こめり 是なんぢの依頼む所ならずや 汝はその道を全うせり 是なんぢの望ならずや
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
請ふ想ひ見よ 誰か罪なくして亡びし者あらん 義者の絶れし事いづくに在や
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
我の觀る所によれば不義を耕へし惡を播く者はその穫る所も亦 是のごとし
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
みな神の氣吹によりて滅びその鼻の息によりて消うす
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
獅子の吼 猛き獅子の聲ともに息み 少き獅子の牙折れ
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
大獅子獲物なくして亡び小獅子散失す
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
前に言の密に我に臨めるありて我その細聲を耳に聞得たり
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
即ち人の熟睡する頃我夜の異象によりて想ひ煩ひをりける時
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
身に恐懼をもよほして戰慄き 骨節ことごとく振ふ
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
時に靈ありて我面の前を過ければ我は身の毛よだちたり
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
その物立とまりしが我はその状を見わかつことえざりき 唯一の物の象わが目の前にあり 時に我しづかなる聲を聞けり云く
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
人いかで神より正義からんや 人いかでその造主より潔からんや
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
彼はその僕をさへに恃みたまはず 其使者をも足ぬ者と見做たまふ
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
況んや土の家に住をりて塵を基とし蜉蝣のごとく亡ぶる者をや
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
是は朝より夕までの間に亡びかへりみる者もなくして永く失逝る
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
その魂の緒あに絶ざらんや皆悟ること無くして死うす

< Ayuba 4 >