< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Elifaz il Temanita prese la parola e disse:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
Se si tenta di parlarti, ti sarà forse gravoso? Ma chi può trattenere il discorso?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Ecco, tu hai istruito molti e a mani fiacche hai ridato vigore;
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
le tue parole hanno sorretto chi vacillava e le ginocchia che si piegavano hai rafforzato.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Ma ora questo accade a te e ti abbatti; capita a te e ne sei sconvolto.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
La tua pietà non era forse la tua fiducia e la tua condotta integra, la tua speranza?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Ricordalo: quale innocente è mai perito e quando mai furon distrutti gli uomini retti?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Per quanto io ho visto, chi coltiva iniquità, chi semina affanni, li raccoglie.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
A un soffio di Dio periscono e dallo sfogo della sua ira sono annientati.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Il ruggito del leone e l'urlo del leopardo e i denti dei leoncelli sono frantumati.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
Il leone è perito per mancanza di preda e i figli della leonessa sono stati dispersi.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
A me fu recata, furtiva, una parola e il mio orecchio ne percepì il lieve sussurro.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Nei fantasmi, tra visioni notturne, quando grava sugli uomini il sonno,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
terrore mi prese e spavento e tutte le ossa mi fece tremare;
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
un vento mi passò sulla faccia, e il pelo si drizzò sulla mia carne...
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Stava là ritto uno, di cui non riconobbi l'aspetto, un fantasma stava davanti ai miei occhi... Un sussurro..., e una voce mi si fece sentire:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
«Può il mortale essere giusto davanti a Dio o innocente l'uomo davanti al suo creatore?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Ecco, dei suoi servi egli non si fida e ai suoi angeli imputa difetti;
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
quanto più a chi abita case di fango, che nella polvere hanno il loro fondamento! Come tarlo sono schiacciati,
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
annientati fra il mattino e la sera: senza che nessuno ci badi, periscono per sempre.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
La funicella della loro tenda non viene forse strappata? Muoiono senza saggezza!».

< Ayuba 4 >