< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Alors Eliphas Témanite prit la parole, et dit:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
Si nous entreprenons de te parler, te fâcheras-tu? mais qui pourrait s'empêcher de parler?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Voilà, tu en as enseigné plusieurs, et tu as renforcé les mains lâches.
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Tes paroles ont affermi ceux qui chancelaient, et tu as fortifié les genoux qui pliaient.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Et maintenant que ceci t'est arrivé, tu t'en fâches! il t'a atteint, et tu en es tout troublé.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Ta piété n'a-t-elle pas été ton espérance? et l'intégrité de tes voies [n'a-t-elle pas été] ton attente?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Rappelle, je te prie, dans ton souvenir, où est l'innocent qui ait jamais péri, et où les hommes droits ont-ils [jamais] été exterminés?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Mais j'ai vu que ceux qui labourent l'iniquité, et qui sèment l'outrage, les moissonnent.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Ils périssent par le souffle de Dieu, et ils sont consumés par le vent de ses narines.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
[Il étouffe] le rugissement du lion, et le cri d'un grand lion, et il arrache les dents des lionceaux.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
Le lion périt par faute de proie, et les petits du vieux lion sont dissipés.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Mais quant à moi, une parole m'a été adressée en secret, et mon oreille en a entendu quelque peu.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Pendant les pensées diverses des visions de la nuit, quand un profond sommeil saisit les hommes,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Une frayeur et un tremblement me saisirent qui étonnèrent tous mes os.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Un esprit passa devant moi, [et] mes cheveux en furent tout hérissés.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Il se tint là, mais je ne connus point son visage; une représentation était devant mes yeux, et j'ouïs une voix basse [qui disait]:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
L'homme sera-t-il plus juste que Dieu? l'homme sera-t-il plus pur que celui qui l'a fait?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Voici, il ne s'assure point sur ses serviteurs, et il met la lumière dans ses Anges:
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
Combien moins [s'assurera-t-il] en ceux qui demeurent dans des maisons d'argile; en ceux dont le fondement est dans la poussière, et qui sont consumés à la rencontre d'un vermisseau?
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Du matin au soir ils sont brisés, et, sans qu'on s'en aperçoive, ils périssent pour toujours.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
L'excellence qui était en eux, n'a-t-elle pas été emportée? Ils meurent sans être sages.

< Ayuba 4 >