< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Éliphaz de Théman prit la parole et dit:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
Si nous osons ouvrir la bouche, en seras-tu peiné? Mais qui pourrait garder le silence?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Voici, tu as souvent enseigné les autres, Tu as fortifié les mains languissantes,
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Tes paroles ont relevé ceux qui chancelaient, Tu as affermi les genoux qui pliaient.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Et maintenant qu’il s’agit de toi, tu faiblis! Maintenant que tu es atteint, tu te troubles!
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Ta crainte de Dieu n’est-elle pas ton soutien? Ton espérance, n’est-ce pas ton intégrité?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Cherche dans ton souvenir: quel est l’innocent qui a péri? Quels sont les justes qui ont été exterminés?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Pour moi, je l’ai vu, ceux qui labourent l’iniquité Et qui sèment l’injustice en moissonnent les fruits;
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Ils périssent par le souffle de Dieu, Ils sont consumés par le vent de sa colère,
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Le rugissement des lions prend fin, Les dents des lionceaux sont brisées;
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
Le lion périt faute de proie, Et les petits de la lionne se dispersent.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Une parole est arrivée furtivement jusqu’à moi, Et mon oreille en a recueilli les sons légers.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Au moment où les visions de la nuit agitent la pensée, Quand les hommes sont livrés à un profond sommeil,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Je fus saisi de frayeur et d’épouvante, Et tous mes os tremblèrent.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Un esprit passa près de moi… Tous mes cheveux se hérissèrent…
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Une figure d’un aspect inconnu était devant mes yeux, Et j’entendis une voix qui murmurait doucement:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
L’homme serait-il juste devant Dieu? Serait-il pur devant celui qui l’a fait?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Si Dieu n’a pas confiance en ses serviteurs, S’il trouve de la folie chez ses anges,
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
Combien plus chez ceux qui habitent des maisons d’argile, Qui tirent leur origine de la poussière, Et qui peuvent être écrasés comme un vermisseau!
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Du matin au soir ils sont brisés, Ils périssent pour toujours, et nul n’y prend garde;
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Le fil de leur vie est coupé, Ils meurent, et ils n’ont pas acquis la sagesse.

< Ayuba 4 >