< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Alors Eliphaz de Théman prit la parole et dit:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
Si nous risquons un mot, peut-être en seras-tu affligé; mais qui pourrait retenir ses paroles?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Voilà que tu en as instruit plusieurs, que tu as fortifié les mains débiles,
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
que tes paroles ont relevé ceux qui chancelaient, que tu as raffermi les genoux vacillants!...
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Et maintenant que le malheur vient à toi, tu faiblis; maintenant qu’il t’atteint, tu perds courage!...
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Ta crainte de Dieu n’était-elle pas ton espoir? Ta confiance n’était-elle pas dans la pureté de ta vie?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Cherche dans ton souvenir: quel est l’innocent qui a péri? En quel lieu du monde les justes ont-ils été exterminés?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Pour moi, je l’ai vu, ceux qui labourent l’iniquité et qui sèment l’injustice, en moissonnent les fruits.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Au souffle de Dieu ils périssent, ils sont consumés par le vent de sa colère.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Le rugissement du lion et sa voix tonnante sont étouffés, et les dents du jeune lion sont brisées;
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
le lion périt faute de proie, et les petits de la lionne se dispersent.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Une parole est arrivée furtivement jusqu’à moi, et mon oreille en a saisi le léger murmure.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Dans le vague des visions de la nuit, à l’heure où un sommeil profond pèse sur les mortels,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
une frayeur et un tremblement me saisirent, et agitèrent tous mes os.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Un esprit passait devant moi... Les poils de ma chair se hérissèrent.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Il se dressa, — je ne reconnus pas son visage, — comme un spectre sous mes yeux. Un grand silence, puis j’entendis une voix:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
L’homme sera-t-il juste vis-à-vis de Dieu? Un mortel sera-t-il pur en face de son Créateur?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Voici qu’il ne se fie pas à ses serviteurs, et qu’il découvre des fautes dans ses anges:
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
combien plus en ceux qui habitent des maisons de boue, qui ont leurs fondements dans la poussière, qui seront réduits en poudre, comme par la teigne!
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Du matin au soir ils sont exterminés, et sans que nul y prenne garde, ils périssent pour jamais.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
La corde de leur tente est coupée, ils meurent avant d’avoir connu la sagesse.

< Ayuba 4 >