< Ayuba 4 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Alors Éliphaz, le Thémanite, prit la parole,
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
« Si quelqu'un s'aventure à parler avec toi, seras-tu affligé? Mais qui peut se retenir de parler?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Voici, vous avez instruit beaucoup de gens, vous avez renforcé les mains faibles.
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Tes paroles ont soutenu celui qui tombait, tu as raffermi les genoux faibles.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Mais maintenant, cela t'est arrivé, et tu t'es évanoui. Il vous touche, et vous êtes troublé.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Votre piété n'est-elle pas votre confiance? L'intégrité de vos voies n'est-elle pas votre espoir?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
« Souviens-toi maintenant de celui qui a péri, étant innocent? Ou bien où ont été coupés les montants?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Selon ce que j'ai vu, ceux qui labourent l'iniquité qui sèment le trouble, récoltent la même chose.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Par le souffle de Dieu, ils périssent. Ils sont consumés par le souffle de sa colère.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Le rugissement du lion, et la voix du lion féroce, les dents des jeunes lions, sont cassées.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
Le vieux lion périt par manque de proie. Les petits de la lionne sont dispersés.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
« Or, une chose m'a été rapportée en secret. Mon oreille en a reçu un murmure.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Dans les pensées des visions de la nuit, quand le sommeil profond tombe sur les hommes,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
La peur m'a saisi, et le tremblement, qui a fait trembler tous mes os.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Alors un esprit passa devant ma face. Les poils de ma chair se sont dressés.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Elle était immobile, mais je ne pouvais pas discerner son apparence. Une forme était devant mes yeux. Silence, puis j'ai entendu une voix, disant,
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
« Un homme mortel serait-il plus juste que Dieu? Un homme peut-il être plus pur que son créateur?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Voici, il ne fait pas confiance à ses serviteurs. Il charge ses anges d'erreurs.
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
Combien plus ceux qui habitent des maisons d'argile, dont les fondations sont dans la poussière, qui sont écrasés par la mite!
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Entre le matin et le soir, ils sont détruits. Ils périssent à jamais sans que personne ne s'en aperçoive.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Leur corde de tente n'est-elle pas arrachée en eux? Ils meurent, et cela sans sagesse.