< Ayuba 4 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Silloin teemanilainen Elifas lausui ja sanoi:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
"Ethän pane pahaksesi, jos sinulle puhutaan? Kuka voi vaitikaan olla?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Katso, monta sinä olet ojentanut, ja hervonneita käsiä olet vahvistanut;
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
sanasi ovat nostaneet kompastunutta, ja rauenneita polvia olet voimistanut.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Mutta nyt, kun itseäsi kova kohtaa, sinä tuskastut, kun se sinuun sattuu, sinä kauhistut.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Eikö jumalanpelkosi ole sinun uskalluksesi ja nuhteeton vaelluksesi sinun toivosi?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Ajattele, kuka viaton on koskaan hukkunut, ja missä ovat rehelliset joutuneet perikatoon?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Minkä minä olen nähnyt, niin ne, jotka vääryyttä kyntävät ja turmiota kylvävät, ne sitä niittävätkin.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Jumalan henkäyksestä he hukkuvat, hänen vihansa hengestä he häviävät.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Leijonan ärjyntä, jalopeuran ääni vaiennetaan, ja nuorten leijonain hampaat murskataan;
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
jalopeura menehtyy saaliin puutteesta, ja naarasleijonan pennut hajaantuvat.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Ja minulle tuli salaa sana, korvani kuuli kuiskauksen,
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
kun ajatukset liikkuivat öisissä näyissä, kun raskas uni oli vallannut ihmiset.
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Pelko ja vavistus yllättivät minut, peljästyttivät kaikki minun luuni.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Tuulen henkäys hiveli kasvojani, ihoni karvat nousivat pystyyn.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Siinä seisoi-sen näköä en erottanut-haamu minun silmäini edessä; minä kuulin kuiskaavan äänen:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
'Onko ihminen vanhurskas Jumalan edessä, onko mies Luojansa edessä puhdas?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Katso, palvelijoihinsakaan hän ei luota, enkeleissäänkin hän havaitsee vikoja;
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
saati niissä, jotka savimajoissa asuvat, joiden perustus on maan tomussa! He rusentuvat kuin koiperhonen;
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
ennenkuin aamu ehtooksi muuttuu, heidät muserretaan. Kenenkään huomaamatta he hukkuvat ainiaaksi.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Eikö niin: heidän telttanuoransa irroitetaan, ja he kuolevat, viisaudesta osattomina.'"