< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then Eliphaz, from Teman, replied to Job. He said,
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
“Will you please let me say something to you? I am not [RHQ] able to remain silent [any longer].
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
In the past, you have instructed/taught many people, and you have encouraged those who were weak.
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
By what you said, you have helped those who (needed spiritual help/almost quit trusting in God) [MET], and you have enabled them to become spiritually strong again [MET].
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
But now, when you experience disasters, you become discouraged. The disasters hit you, and you are stunned.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
You revere God; (does that not cause you to trust [in him]?/that should cause you to trust [in him].) [RHQ] If you were guiltless, you would [RHQ] be confident that [God] would not [have allowed] these disasters [to] happen to you!
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Think about this: Do innocent people die [while they are still young] [RHQ]? Does God get rid of godly people [RHQ]? [No!]
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
What I have experienced is this: [Just as] [MET] farmers who plant bad [seeds] do not harvest good [crops], [just as those who start] trouble for others, later bring trouble on themselves.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
They die when God angrily blows his breath on them, when he is very angry with them.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
[Even though wicked people may be very powerful like] young lions, [God] will get rid of them [MET].
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
[They will die like] fierce lions [that] starve to death when there are no animals that they can kill and eat, and [their children will be separated from each other like] young lions separate from each other [to find food].”
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
“I heard a message that someone came and whispered to me.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
He spoke to me at night when I was having a bad dream that disturbed/frightened me while I was fast asleep.
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
It caused me to be afraid and tremble; it caused all my bones to shake.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
A ghost glided past my face and caused the hair on [on the back of] my neck to stand straight up.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
It stopped, but I could not see what form it had. But [I could sense that] there was some being in front of me, and it said in a quiet voice,
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
‘(Does God consider anyone to be righteous?/No human beings can be righteous in God’s sight!) [RHQ] (Their creator cannot consider them to be pure./Can their creator consider them to be pure?) [RHQ]
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
God cannot be sure that his own angels [will always do what is right]; he declares that some of them have done what is wrong.
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
So he certainly cannot trust human beings who were made from dust and clay, who are crushed as easily as moths are crushed!
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
People are sometimes well in the morning, but in the evening they are dead. They are gone forever and do not even know it (OR, and no one pays any attention to it).
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
They are like [MET] tents that collapse [suddenly]: They die [suddenly] before they become wise.’”

< Ayuba 4 >