< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
And he answered Eliphaz the Temanite and he said.
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
¿ Did someone attempt a word to you will you be impatient? and to restrain words who? is he able.
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
There! you have instructed many [people] and hands slack you strengthened.
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
[the] stumbling They raised! words your and knees bending you strengthened.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
For now - it comes to you and you have become impatient it reaches to you and you have become dismayed.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
¿ Not [is] fear your confidence your hope your and [the] integrity of ways your.
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Remember please who? that innocent did he perish and where? upright [people] were they destroyed.
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Just as I have seen plowers of wickedness and sowers of mischief they harvest it.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
From [the] breath of God they perish and from [the] breath of anger his they come to an end.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
[the] roaring of A lion and [the] sound of a lion and [the] teeth of young lions they are broken out.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
A lion [is] perishing because not prey and [the] young of a lion they are scattered.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
And to me a word it was brought secretly and it received ear my a whisper of it.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
In disquieting thoughts from visions of [the] night when falls deep sleep on people.
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Fear it happened to me and trembling and [the] multitude of bones my it caused to tremble.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
And a wind over face my it passed over it made bristle [the] hair of flesh my.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
It stood still - and not I recognized appearance its a form [was] to before eyes my a whisper and a voice I heard.
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
¿ A person from God will he be righteous or? from maker his will he be pure a man.
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
There! in servants his not he trusts and against messengers his he charges error.
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
Also - [those who] dwell of houses of clay which [is] in the dust foundation their people crush them before a moth.
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
From morning to evening they are crushed to pieces because not [one who] sets to perpetuity they perish.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
¿ Not has it been pulled up tent cord their in them will they die? and not with wisdom.

< Ayuba 4 >