< Ayuba 4 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then Eliphaz the Themanite answered, and said:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
If we begin to speak to thee, perhaps thou wilt take it ill, but who can withhold the words he hath conceived?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Behold thou hast taught many, and thou hast strengthened the weary hands:
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Thy words have confirmed them that were staggering, and thou hast strengthened the trembling knees:
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
But now the scourge is come upon thee, and thou faintest: it hath touched thee, and thou art troubled.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Where is thy fear, thy fortitude, thy patience, and the perfection of thy ways?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Remember, I pray thee, who ever perished being innocent? or when were the just destroyed?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
On the contrary I have seen those who work iniquity, and sow sorrows, and reap them,
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Perishing by the blast of God, and consumed by the spirit of his wrath.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
The roaring of the lion, and the voice of the lioness, and the teeth of the whelps of lions are broken:
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
The tiger hath perished for want of prey, and the young lions are scattered abroad.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Now there was a word spoken to me in private, and my ears by stealth as it were received the veins of its whisper.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
In the horror of a vision by night, when deep sleep is wont to hold men,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Fear seized upon me, and trembling, and all my bones were affrighted:
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
And when a spirit passed before me, the hair of my flesh stood up.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
There stood one whose countenance I knew not, an image before my eyes, and I heard the voice as it were of a gentle wind:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
Shall man be justified in comparison of God, or shall a man be more pure than his maker?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Behold they that serve him are not steadfast, and in his angels he found wickedness:
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
How much more shall they that dwell in houses of clay, who have an earthly foundation, be consumed as with the moth?
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
From morning till evening they shall be cut down: and because no one understandeth, they shall perish for ever.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
And they that shall be left, shall be taken away from them: they shall die, and not in wisdom.