< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
¿Sabes tú el tiempo en que paren las cabras monteses? ¿ó miraste tú las ciervas cuando están pariendo?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
¿Contaste tú los meses de su preñez, y sabes el tiempo cuando han de parir?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
Encórvanse, hacen salir sus hijos, pasan sus dolores.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Sus hijos están sanos, crecen con el pasto: salen y no vuelven á ellas.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
¿Quién echó libre al asno montés, y quién soltó sus ataduras?
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Al cual yo puse casa en la soledad, y sus moradas en lugares estériles.
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
Búrlase de la multitud de la ciudad: no oye las voces del arriero.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
Lo oculto de los montes es su pasto, y anda buscando todo lo que está verde.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
¿Querrá el unicornio servirte á ti, ni quedar á tu pesebre?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
¿Atarás tú al unicornio con su coyunda para el surco? ¿labrará los valles en pos de ti?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
¿Confiarás tú en él, por ser grande su fortaleza, y le fiarás tu labor?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
¿Fiarás de él que te tornará tu simiente, y que [la] allegará en tu era?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
¿[Diste tú] hermosas alas al pavo real, ó alas y plumas al avestruz?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
El cual desampara en la tierra sus huevos, y sobre el polvo los calienta,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
Y olvídase de que los pisará el pie, y que los quebrará bestia del campo.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Endurécese para con sus hijos, como si no fuesen suyos, no temiendo que su trabajo haya sido en vano:
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Porque le privó Dios de sabiduría, y no le dió inteligencia.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
Luego que se levanta en alto, búrlase del caballo y de su jinete.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
¿Diste tú al caballo la fortaleza? ¿vestiste tú su cerviz de relincho?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
¿Le intimidarás tú como á alguna langosta? El resoplido de su nariz es formidable:
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
Escarba la tierra, alégrase en su fuerza, sale al encuentro de las armas:
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
Hace burla del espanto, y no teme, ni vuelve el rostro delante de la espada.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Contra él suena la aljaba, el hierro de la lanza y de la pica:
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
Y él con ímpetu y furor escarba la tierra, sin importarle el sonido de la bocina;
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
[Antes como] que dice entre los clarines: ¡Ea!, y desde lejos huele la batalla, el grito de los capitanes, y la vocería.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
¿Vuela el gavilán por tu industria, y extiende hacia el mediodía sus alas?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
¿Se remonta el águila por tu mandamiento, y pone en alto su nido?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
Ella habita y está en la piedra, en la cumbre del peñasco y de la roca.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
Desde allí acecha la comida: sus ojos observan de muy lejos.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Sus pollos chupan la sangre: y donde hubiere cadáveres, allí está.

< Ayuba 39 >