< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
"Vielleicht kennst du der Gemsen Werfen? Acht gibst du auf der Hirschkuh Kreißen?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Die Monde zählst du, die sie trächtig gehen? Die Zeit weißt du, da sie gebären?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
Sie krümmen sich und trennen selber ihre Schnüre und machen ihren Nachwuchs frei.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Und ihre Jungen werden stark; im Freien wachsen sie; sie laufen fort und kehren nimmermehr zurück.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Wer hat den wilden Esel freigelassen? Wer ließ den Wildfang in die Freiheit,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
dem ich die Wüste zur Behausung gab, die Salzsteppe zur Wohnung?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
Er spottet des Getöses in der Stadt; der Treiber Lärmen hört er nicht.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
Was auf den Bergen er erspäht, ist seine Weide, und allem Grünen spürt er nach.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Wird dir der Wildochs willig dienen? Und nächtigt er an deiner Krippe?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Kannst du den Wildochsen an einen Zugstrick binden? Wird er, dir folgend, in den Tälern Gründe eggen?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Verläßt du dich auf ihn, weil seine Kraft so groß, und überlässest du ihm deine Ernte?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Wirst du ihm zutrauen, daß er auch dresche und deine Saaternte heimbringen helfe?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
Des Straußes Flügel schlägt gar übermütig. Wennschon ein Storch nach Schwingen und nach Federn,
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
so überläßt er doch der Erde seine Eier und läßt sie auf dem Boden wärmen.
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
Und er vergißt, daß sie ein Fuß zertreten, das Wild der Steppe sie zerdrücken könnte.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Und er behandelt seine Jungen hart, als ob sie nicht die seinen wären, ganz sorglos, ob umsonst nicht seine Mühe.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Denn Gott hat Klugheit ihm versagt und keinen Anteil an Verstand gegeben,
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
sonst würde er an hochgelegenen Orten brüten und so des Rosses und des Reiters spotten. -
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Verleihst du wohl dem Rosse Heldenkraft, bekleidest seinen Hals mit einer Mähne,
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
bewirkst du, daß es wie ein Rauchfang dampfe? Erschreckend ist sein mächtig Wiehern.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
Voll Freude springt es in das Tal; voll Kraft stürzt es den Harnischen entgegen.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
Des Schreckens lacht's, hat keine Angst und macht nicht kehrt vorm Schwerte.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Der Köcher klirrt auf ihm, der Speer, der blitzende, die Lanze.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
Mit Toben und mit Ungestüm scharrt's auf dem Boden, hält nimmer fest, tönt die Trompete.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
Bei dem Trompetenklang ruft's: 'Hui!' Von ferne wittert es den Streit, der Fahrer Donnerruf, das Schlachtgeschrei.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Nach deinem Gutdünken zieht wohl der Habicht fort und breitet nach dem Süden seine Flügel aus?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Auf dein Geheiß fliegt wohl so hoch der Adler und nistet in der Höhe?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
Er wohnt und horstet auf dem Felsen, auf Felsenzacken, auf der hohen Wacht.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
Von dort erspäht er sich den Fraß; in weite Fernen blicken seine Augen.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Und seine Brut stürzt sich auf Blut; wo Leichen sind, da ist auch er."

< Ayuba 39 >