< Ayuba 39 >
1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Knowest thou the season when the Wild Goats of the crags beget? The bringing forth of the hinds, canst thou observe?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Canst thou count the months they fulfil? Or knowest thou the time when they give birth?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They kneel down, their young, they bring forth; their pains, they throw off;
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Their young become strong, they grow up in the open field, they go out, and return not unto them.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Who hath sent forth the Wild Ass free? And, the bands of the swift-runner, who hath loosed?
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Whose house I have made the waste plain, and his dwellings, the land of salt:
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He laugheth at the throng of the city, The shoutings of the driver, he heareth not;
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
He espieth the mountains, his pasture-ground, and, after every green thing, maketh search.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Will the Wild-Ox be pleased to be thy servant? or lodge for the night by thy crib?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Canst thou bind the wild-ox, so that—with the ridge—shall run his cord? Or will he harrow the furrows after thee?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Wilt thou trust in him, because of the greatness of his strength? Wilt thou leave unto him thy toil?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Wilt thou put faith in him, that he will bring back thy seed? and that, corn for thy threshing-floor, he will gather?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
The wing of the Ostrich that waveth itself joyfully, Is it the pinion of lovingkindness or the plumage?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
For she leaveth—to the earth—her eggs, and, on the dust, she letteth them be warmed;
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
And hath forgotten, that, a foot, may crush them, —or, the wild beast, tread on them!
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Dealing hardly with her young, as none-of-hers, In vain, her labour, without dread.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
For GOD hath suffered her to forget wisdom, and given her no share in understanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
What time, on high, she vibrateth her wings, she laugheth at the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Couldst thou give—to the Horse—strength? Couldst thou clothe his neck with the quivering mane?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Couldst thou cause him to leap like a locust? The majesty of his snort, is a terror!
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He diggeth into the plain, and rejoiceth in vigour, he goeth forth to meet armour;
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He laugheth at dread, and is not dismayed, neither turneth he back, from the face of the sword;
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Against him, whiz [the arrows of] the quiver, the flashing head of spear and javelin;
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
With stamping and rage, he drinketh up the ground, —he will not stand still when the horn soundeth;
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
As oft as the horn soundeth, he saith, Aha! And, from afar, he scenteth the battle, —the thunder of commanders and the war-cry.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Is it, by thine understanding, that the Bird of Passage betaketh him to his pinions? spreadeth out his wings to the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Or, at thy bidding, that the Eagle mounteth, and that he setteth on high his nest?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
The crag, he inhabiteth, and so lodgeth himself, on the tooth of the crag, and high fort;
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From thence, he searcheth out food, far away, his eyes do pierce;
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
And, his young brood, suck up blood, and, where the slain are, there, is he.