< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Knowest thou the time when the wilde goates bring foorth yong? or doest thou marke when the hindes doe calue?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Canst thou nomber the moneths that they fulfill? or knowest thou the time when they bring foorth?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They bow them selues: they bruise their yong and cast out their sorowes.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Yet their yong waxe fatte, and growe vp with corne: they goe foorth and returne not vnto them.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Who hath set the wilde asse at libertie? or who hath loosed the bondes of the wilde asse?
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
It is I which haue made the wildernesse his house, and the salt places his dwellings.
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He derideth the multitude of the citie: he heareth not the crie of the driuer.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
He seeketh out the mountaine for his pasture, and searcheth after euery greene thing.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Will the vnicorne serue thee? or will he tary by thy cribbe?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Canst thou binde the vnicorne with his band to labour in the furrowe? or will he plowe the valleyes after thee?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Wilt thou trust in him, because his strength is great, and cast off thy labour vnto him?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Wilt thou beleeue him, that he will bring home thy seede, and gather it vnto thy barne?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
Hast thou giuen the pleasant wings vnto the peacockes? or winges and feathers vnto the ostriche?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
Which leaueth his egges in the earth, and maketh them hote in the dust,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
And forgetteth that the foote might scatter the, or that the wild beast might breake the.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
He sheweth himselfe cruell vnto his yong ones, as they were not his, and is without feare, as if he trauailed in vaine.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
For God had depriued him of wisedom, and hath giuen him no part of vnderstanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
When time is, he mounteth on hie: he mocketh the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Hast thou giuen the horse strength? or couered his necke with neying?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Hast thou made him afraid as the grashopper? his strong neying is fearefull.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He diggeth in the valley, and reioyceth in his strength: he goeth foorth to meete the harnest man.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He mocketh at feare, and is not afraid, and turneth not backe from the sworde,
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Though the quiuer rattle against him, the glittering speare and the shield.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
He swalloweth the ground for fearcenes and rage, and he beleeueth not that it is the noise of the trumpet.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
He sayth among the trumpets, Ha, ha: hee smellleth the battell afarre off, and the noyse of the captaines, and the shouting.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Shall the hauke flie by thy wisedome, stretching out his wings toward the South?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Doeth the eagle mount vp at thy commandement, or make his nest on hie?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
Shee abideth and remaineth in the rocke, euen vpon the toppe of the rocke, and the tower.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From thence she spieth for meate, and her eyes beholde afarre off.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
His young ones also sucke vp blood: and where the slaine are, there is she.

< Ayuba 39 >