< Ayuba 39 >
1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Knowest thou the time when the wild goats bring forth among the rocks, or hast thou observed the hinds when they fawn?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Hast thou numbered the months of their conceiving, or knowest thou the time when they bring forth?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They bow themselves to bring forth young, and they cast them, and send forth roarings.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Their young are weaned and go to feed: they go forth, and return not to them.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Who hath sent out the wild ass free, and who hath loosed his bonds?
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
To whom I have given a house in the wilderness, and his dwellings in the barren land.
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He scorneth the multitude of the city, he heareth not the cry of the driver.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
He looketh round about the mountains of his pasture, and seeketh for every green thing.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Shall the rhinoceros be willing to serve thee, or will he stay at thy crib?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Canst thou bind the rhinoceros with thy thong to plough, or will he break the clods of the valleys after thee?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Wilt thou have confidence in his great strength, and leave thy labours to him?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Wilt thou trust him that he will render thee the seed, and gather it into thy barnfloor?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
The wing of the ostrich is like the wings of the heron, and of the hawk.
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
When she leaveth her eggs on the earth, thou perhaps wilt warm them in the dust.
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
She forgetteth that the foot may tread upon them, or that the beasts of the field may break them.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
She is hardened against her young ones, as though they were not hers, she hath laboured in vain, no fear constraining her.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
For God hath deprived her of wisdom, neither hath he given her understanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
When time shall be, she setteth up her wings on high: she scorneth the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Wilt thou give strength to the horse, or clothe his neck with neighing?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Wilt thou lift him up like the locusts? the glory of his nostrils is terror.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He breaketh up the earth with his hoof, he pranceth boldly, he goeth forward to meet armed men.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He despiseth fear, he turneth not his back to the sword,
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Above him shall the quiver rattle, the spear and shield shall glitter.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
Chasing and raging he swalloweth the ground, neither doth he make account when the noise of the trumpet soundeth.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
When he heareth the trumpet he saith: Ha, ha: he smelleth the battle afar off, the encouraging of the captains, and the shouting of the army.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Doth the hawk wax feathered by thy wisdom, spreading her wings to the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Will the eagle mount up at thy command, and make her nest in high places?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
She abideth among the rocks, and dwelleth among cragged flints, and stony hills, where there is no access.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From thence she looketh for the prey, and her eyes behold afar off.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Her young ones shall suck up blood: and wheresoever the carcass shall be, she is immediately there.