< Ayuba 39 >
1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Knowest thou the time when the wild goats of the rock bring forth? dost thou mark the calving of the hinds?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Dost thou number the months that they fulfil? and knowest thou the time when they bring forth?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They bow themselves, they give birth to their young ones, they cast out their pains;
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Their young ones become strong, they grow up in the open field, they go forth, and return not unto them.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Who hath sent out the wild ass free? and who hath loosed the bands of the onager,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Whose house I made the wilderness, and the salt plain his dwellings?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He laugheth at the tumult of the city, and heareth not the shouts of the driver;
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
The range of the mountains is his pasture, and he searcheth after every green thing.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Will the buffalo be willing to serve thee, or will he lodge by thy crib?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Canst thou bind the buffalo with his cord in the furrow? or will he harrow the valleys after thee?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Wilt thou put confidence in him, because his strength is great? and wilt thou leave thy labour to him?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Wilt thou trust him to bring home thy seed, and gather it into thy threshing-floor?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
The wing of the ostrich beats joyously — But is it the stork's pinion and plumage?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
For she leaveth her eggs to the earth, and warmeth them in the dust,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
And forgetteth that the foot may crush them, or that the beast of the field may trample them.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
She is hardened against her young ones, as though they were not hers; her labour is in vain, without her concern.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
For God hath deprived her of wisdom, and hath not furnished her with understanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
What time she lasheth herself on high, she scorneth the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Hast thou given strength to the horse? hast thou clothed his neck with the quivering mane?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Dost thou make him to leap as a locust? His majestic snorting is terrible.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He paweth in the valley, and rejoiceth in [his] strength; he goeth forth to meet the armed host.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He laugheth at fear, and is not affrighted; neither turneth he back from before the sword.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
The quiver rattleth upon him, the glittering spear and the javelin.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
He swalloweth the ground with fierceness and rage, and cannot contain himself at the sound of the trumpet:
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
At the noise of the trumpets he saith, Aha! and he smelleth the battle afar off, the thunder of the captains, and the shouting.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Doth the hawk fly by thine intelligence, [and] stretch his wings toward the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Doth the eagle mount up at thy command, and make his nest on high?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
He inhabiteth the rock and maketh his dwelling on the point of the cliff, and the fastness:
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From thence he spieth out the prey, his eyes look into the distance;
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
And his young ones suck up blood; and where the slain are, there is he.