< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Knowest thou the time when the wild goats of the rock bring forth? [Or] canst thou mark when the hinds do calve?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Canst thou number the months that they fulfil? Or knowest thou the time when they bring forth?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They bow themselves, they bring forth their young, They cast out their pains.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Their young ones become strong, they grow up in the open field; They go forth, and return not again.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Who hath sent out the wild ass free? Or who hath loosed the bonds of the swift ass,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Whose home I have made the wilderness, And the salt land his dwelling-place?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He scorneth the tumult of the city, Neither heareth he the shoutings of the driver.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
The range of the mountains is his pasture, And he searcheth after every green thing.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Will the wild-ox be content to serve thee? Or will he abide by thy crib?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Canst thou bind the wild-ox with his band in the furrow? Or will he harrow the valleys after thee?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Wilt thou trust him, because his strength is great? Or wilt thou leave to him thy labor?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Wilt thou confide in him, that he will bring home thy seed, And gather [the grain] of thy threshing-floor?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
The wings of the ostrich wave proudly; [But] are they the pinions and plumage of love?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
For she leaveth her eggs on the earth, And warmeth them in the dust,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
And forgetteth that the foot may crush them, Or that the wild beast may trample them.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
She dealeth hardly with her young ones, as if they were not hers: Though her labor be in vain, [she is] without fear;
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Because God hath deprived her of wisdom, Neither hath he imparted to her understanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
What time she lifteth up herself on high, She scorneth the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Hast thou given the horse [his] might? Hast thou clothed his neck with the quivering mane?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Hast thou made him to leap as a locust? The glory of his snorting is terrible.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He paweth in the valley, and rejoiceth in his strength: He goeth out to meet the armed men.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He mocketh at fear, and is not dismayed; Neither turneth he back from the sword.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
The quiver rattleth against him, The flashing spear and the javelin.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
He swalloweth the ground with fierceness and rage; Neither believeth he that it is the voice of the trumpet.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
As oft as the trumpet [soundeth] he saith, Aha! And he smelleth the battle afar off, The thunder of the captains, and the shouting.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Is it by thy wisdom that the hawk soareth, [And] stretcheth her wings toward the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Is it at thy command that the eagle mounteth up, And maketh her nest on high?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
On the cliff she dwelleth, and maketh her home, Upon the point of the cliff, and the stronghold.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From thence she spieth out the prey; Her eyes behold it afar off.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Her young ones also suck up blood: And where the slain are, there is she.

< Ayuba 39 >