< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Y el Señor respondió a Job desde el viento de tormenta, y dijo:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
¿Quién es este que hace que el consejo de Dios sea oscuro por palabras sin conocimiento?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Reúne tus fuerzas como un hombre de guerra; Te haré preguntas y tú me darás las respuestas.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
¿Dónde estabas cuando puse la tierra en su base? Dimelo, si tienes conocimiento.
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
¿Por quién fueron fijadas sus medidas? si tienes sabiduría; ¿O por quién se extendía la línea sobre ella?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
¿En qué se basaron sus pilares, o quién dejó su piedra angular,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
¿Cuando las estrellas de la mañana hicieron canciones juntas, y todos los hijos de Dios dieron gritos de alegría?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
¿O dónde estabas cuando nació el mar, saliendo de su lugar secreto;
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
Cuando hice la túnica de la nube y puse nubes gruesas como faja alrededor de ella.
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
Ordenando un límite fijo para ello, con cerraduras y puertas;
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
Y dijo: Hasta aquí puedes llegar, y no más allá; ¿Y aquí se detendrá el orgullo de tus olas?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
¿Has dado órdenes desde la madrugada hasta la mañana o has hecho consciente a la aurora de su lugar?
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
¿Para que pueda difundir su luz a la tierra, sacudiendo a todos los que hacen el mal?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
Se cambia como barro bajo un sello, y se colorea como una túnica;
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
Y de los malhechores es quitada su luz, y se rompe el brazo del orgulloso.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
¿Has venido a los manantiales del mar, caminando en los lugares secretos de las profundidades?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
¿Te han abierto las puertas de la muerte, o te han visto los guardianes de las puertas de la oscuridad?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
¿Has tomado nota de los amplios límites de la tierra? Declara, si tienes conocimiento de todo.
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Cuál es camino donde mora la luz y las tinieblas. Donde es este lugar?
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
Para que lo lleves a su límite, y entenderás el camino a su casa.
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Sin duda tienes conocimiento de ello, pues entonces naciste y el número de tus días es grande.
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
¿Has venido al lugar secreto de la nieve, o has visto los almacenes del granizo,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
¿Qué he guardado para el tiempo de angustia, para el día de la guerra y la lucha?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
¿Cuál es el camino a donde se reparte la luz, y el viento del este esparcido sobre la tierra?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
¿Por quién ha sido dividido un canal para él diluvio o un camino para él estruendo del relámpago?
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
Causando que la lluvia caiga en una tierra donde ningún hombre vive, en el desierto que no tiene gente;
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
Dar agua a la tierra donde hay desperdicio y destrucción, y hacer que produzca una fuente de retoños.
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
¿Tiene la lluvia un padre? ¿O quién dio a luz al rocío?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
¿De cuyo cuerpo salió el hielo? ¿Y quién dio a luz a la escarcha del cielo?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
Las aguas se unen, duras como una piedra, y se cubre la faz de la profundidad.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
¿Puedes arreglar un cúmulo de estrellas, o soltar los cordones de Orión?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
¿Haces que las constelaciones salgan en el momento adecuado, o guías a la Osa y sus estrellas?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
¿Tienes conocimiento de las leyes de los cielos? ¿Les diste dominio sobre la tierra?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
¿Puedes alzar tu voz a las nubes para que te inunden las aguas?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
¿Enviar los truenos para que vayan y te digan: “Aquí estamos?”
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
¿Quién ha puesto sabiduría en lo más profundo, o ha dado conocimiento a la mente?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Quien por sabiduría puede contar las nubes, Quién puede inclinarlas para que den lluvia, Quién las hace parar.
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
¿Cuando el polvo se endurece, y los terrones se pegan entre sí?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
¿Buscas comida para él león, o para que sus cachorros sacien su apetito?
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
¿Cuándo están echados en las cuevas, y están esperando en la maleza para acechar?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
¿Quién da a los cuervos por la tarde la carne que está buscando, cuando sus crías están llorando a Dios? Y van vagando sin comida?