< Ayuba 38 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Então o SENHOR respondeu a Jó desde um redemoinho, e disse:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Quem é esse que obscurece o conselho com palavras sem conhecimento?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Agora cinge teus lombos como homem; e eu te perguntarei, e tu me explicarás.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Onde estavas tu quando eu fundava a terra? Declara- [me], se tens inteligência.
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Quem determinou suas medidas, se tu o sabes? Ou quem estendeu cordel sobre ela?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Sobre o que estão fundadas suas bases? Ou quem pôs sua pedra angular,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
Quando as estrelas do amanhecer cantavam alegremente juntas, e todos os filhos de Deus jubilavam?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Ou [quem] encerrou o mar com portas, quando transbordou, saindo da madre,
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
Quando eu pus nuvens por sua vestidura, e a escuridão por sua faixa;
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
Quando eu passei sobre ele meu decreto, e [lhe] pus portas e ferrolhos,
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
E disse: Até aqui virás, e não passarás adiante, e aqui será o limite para a soberba de tuas ondas?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Desde os teus dias tens dado ordem à madrugada? [Ou] mostraste tu ao amanhecer o seu lugar,
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
Para que tomasse os confins da terra, e os perversos fossem sacudidos dela?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
E [a terra] se transforma como barro [sob] o selo; [todas as coisas sobre ela] se apresentam como vestidos?
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
E dos perversos é desviada sua luz, e o braço erguido é quebrado.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Por acaso chegaste tu às fontes do mar, ou passeaste no mais profundo abismo?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Foram reveladas a ti as portas da morte, ou viste as portas da sombra de morte?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Entendeste tu as larguras da terra? Declara, se sabes tudo isto.
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Onde está o caminho [por onde] mora a luz? E quanto às trevas, onde fica o seu lugar?
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
Para que as tragas a seus limites, e conheças os caminhos de sua casa.
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Certamente tu o sabes, pois já eras nascido, e teus dias são inúmeros!
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Por acaso entraste tu aos depósitos da neve, e viste os depósitos do granizo,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
Que eu retenho até o tempo da angústia, até o dia da batalha e da guerra?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Onde está o caminho em que a luz se reparte, e o vento oriental se dispersa sobre a terra?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Quem repartiu um canal às correntezas de águas, e caminho aos relâmpagos dos trovões,
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
Para chover sobre a terra [onde] havia ninguém, [sobre] o deserto, onde não há gente,
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
Para fartar [a terra] deserta e desolada, e para fazer crescer aos renovos da erva.
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Por acaso a chuva tem pai? Ou quem gera as gotas do orvalho?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
De qual ventre procede o gelo? E quem gera a geada do céu?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
As águas se tornam duras como pedra, e a superfície do abismo se congela.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Podes tu atar as cadeias das Plêiades, ou desatar as cordas do Órion?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Podes tu trazer as constelações a seu tempo, e guiar a Ursa com seus filhos?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Sabes tu as ordenanças dos céus? Ou podes tu dispor do domínio deles sobre a terra?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Ou podes levantar tua voz até às nuvens, para que a abundância das águas te cubra?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Podes tu mandar relâmpagos, para que saiam, e te digam: Eis-nos aqui?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Quem pôs a sabedoria no íntimo? Ou quem deu entendimento à mente?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Quem pode enumerar as nuvens com sabedoria? E os odres dos céus, quem pode os despejar?
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
Quando o pó se endurece, e os torrões se apegam uns aos outros?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Caçarás tu a presa para o leão? Ou saciarás a fome dos leões jovens,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
Quando estão agachados nas covas, [ou] estão à espreita no matagal?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Quem prepara aos corvos seu alimento, quando seus filhotes clamam a Deus, andando de um lado para o outro por não terem o que comer?

< Ayuba 38 >