< Ayuba 38 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Og Herren svarte Job ut av et stormvær og sa:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Hvem er han som formørker mitt råd med ord uten forstand?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Nuvel, omgjord dine lender som en mann! Så vil jeg spørre dig, og du skal lære mig.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Hvor var du da jeg grunnfestet jorden? Si frem hvis du vet det!
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Hvem fastsatte vel dens mål? Vet du det? Eller hvem spente målesnor ut over den?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Hvor blev dens støtter rammet ned, eller hvem la dens hjørnesten,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
mens alle morgenstjerner jublet, og alle Guds sønner ropte av fryd?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Og hvem lukket for havet med dører, da det brøt frem og gikk ut av mors liv,
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
da jeg gjorde skyer til dets klædebon og skodde til dets svøp
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
og merket av en grense for det og satte bom og dører
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
og sa: Hit skal du komme og ikke lenger, her skal dine stolte bølger legge sig?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Har du i dine dager befalt morgenen å bryte frem, har du vist morgenrøden dens sted,
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
forat den skulde gripe fatt i jordens ender, og de ugudelige rystes bort fra den?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
Jorden tar da form likesom ler under seglet, og tingene treder frem som et klædebon,
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
og de ugudelige unddras sitt lys, og den løftede arm knuses.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Er du kommet til havets kilder, og har du vandret på dypets bunn?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Har dødens porter vist sig for dig, og har du sett dødsskyggens porter?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Har du sett ut over jordens vidder? Si frem dersom du kjenner alt dette!
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Hvor er veien dit hvor lyset bor? Og mørket - hvor er dets sted,
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
så du kunde hente det frem til dets område, så du kjente stiene til dets hus?
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Du vet det vel; dengang blev du jo født, og dine dagers tall er stort.
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Er du kommet til forrådskammerne for sneen, og har du sett forrådshusene for haglet,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
som jeg har opspart til trengselens tid, til kampens og krigens dag?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Hvad vei følger lyset når det deler sig, og østenvinden når den spreder sig over jorden?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Hvem har åpnet renner for regnskyllet og vei for lynstrålen
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
for å la det regne over et øde land, over en ørken hvor intet menneske bor,
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
for å mette ørk og øde og få gressbunnen til å gro?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Har regnet nogen far? Eller hvem har avlet duggens dråper?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Av hvis liv er vel isen gått frem, og himmelens rim - hvem fødte det?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
Vannet blir hårdt som sten, og havets overflate stivner.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Kan du knytte Syvstjernens bånd, eller kan du løse Orions lenker?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Kan du føre Dyrekretsens stjernebilleder frem i rette tid, og Bjørnen med dens unger - kan du styre deres gang?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Kjenner du himmelens lover? Fastsetter du dens herredømme over jorden?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Kan din røst nå op til skyen, så en flom av vann dekker dig?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Kan du sende ut lynene, så de farer avsted, så de sier til dig: Se, her er vi?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Hvem har lagt visdom i de mørke skyer, eller hvem har lagt forstand i luftsynet?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Hvem teller skyene med visdom, og himmelens vannsekker - hvem heller vannet ut av dem,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
når støvet flyter sammen til en fast masse, og jordklumpene henger fast ved hverandre?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Jager du rov for løvinnen, og metter du de grådige ungløver,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
når de dukker sig ned i sine huler og ligger på lur i krattet?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Hvem lar ravnen finne sin mat, når dens unger skriker til Gud og farer hit og dit uten føde?

< Ayuba 38 >