< Ayuba 38 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Respondens autem Dominus Job de turbine, dixit:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
[Quis est iste involvens sententias sermonibus imperitis?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Accinge sicut vir lumbos tuos: interrogabo te, et responde mihi.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Ubi eras quando ponebam fundamenta terræ? indica mihi, si habes intelligentiam.
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Quis posuit mensuras ejus, si nosti? vel quis tetendit super eam lineam?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Super quo bases illius solidatæ sunt? aut quis demisit lapidem angularem ejus,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
cum me laudarent simul astra matutina, et jubilarent omnes filii Dei?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Quis conclusit ostiis mare, quando erumpebat quasi de vulva procedens;
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
cum ponerem nubem vestimentum ejus, et caligine illud quasi pannis infantiæ obvolverem?
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
Circumdedi illud terminis meis, et posui vectem et ostia,
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
et dixi: Usque huc venies, et non procedes amplius, et hic confringes tumentes fluctus tuos.
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Numquid post ortum tuum præcepisti diluculo, et ostendisti auroræ locum suum?
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
Et tenuisti concutiens extrema terræ, et excussisti impios ex ea?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
Restituetur ut lutum signaculum, et stabit sicut vestimentum:
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
auferetur ab impiis lux sua, et brachium excelsum confringetur.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Numquid ingressus es profunda maris, et in novissimis abyssi deambulasti?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Numquid apertæ sunt tibi portæ mortis, et ostia tenebrosa vidisti?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Numquid considerasti latitudinem terræ? indica mihi, si nosti, omnia:
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
in qua via lux habitet, et tenebrarum quis locus sit:
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
ut ducas unumquodque ad terminos suos, et intelligas semitas domus ejus.
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Sciebas tunc quod nasciturus esses, et numerum dierum tuorum noveras?
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Numquid ingressus es thesauros nivis, aut thesauros grandinis aspexisti,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
quæ præparavi in tempus hostis, in diem pugnæ et belli?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Per quam viam spargitur lux, dividitur æstus super terram?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Quis dedit vehementissimo imbri cursum, et viam sonantis tonitrui,
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
ut plueret super terram absque homine in deserto, ubi nullus mortalium commoratur;
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
ut impleret inviam et desolatam, et produceret herbas virentes?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Quis est pluviæ pater? vel quis genuit stillas roris?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
De cujus utero egressa est glacies? et gelu de cælo quis genuit?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
In similitudinem lapidis aquæ durantur, et superficies abyssi constringitur.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Numquid conjungere valebis micantes stellas Pleiadas, aut gyrum Arcturi poteris dissipare?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Numquid producis luciferum in tempore suo, et vesperum super filios terræ consurgere facis?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Numquid nosti ordinem cæli, et pones rationem ejus in terra?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Numquid elevabis in nebula vocem tuam, et impetus aquarum operiet te?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Numquid mittes fulgura, et ibunt, et revertentia dicent tibi: Adsumus?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Quis posuit in visceribus hominis sapientiam? vel quis dedit gallo intelligentiam?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Quis enarrabit cælorum rationem? et concentum cæli quis dormire faciet?
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
Quando fundebatur pulvis in terra, et glebæ compingebantur?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Numquid capies leænæ prædam, et animam catulorum ejus implebis,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
quando cubant in antris, et in specubus insidiantur?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Quis præparat corvo escam suam, quando pulli ejus clamant ad Deum, vagantes, eo quod non habeant cibos?]

< Ayuba 38 >