< Ayuba 38 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Da antwortete der HERR dem Hiob aus dem Wettersturme heraus folgendermaßen:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
»Wer ist’s, der da den Heilsplan Gottes verdunkelt mit Worten ohne Einsicht?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Auf! Gürte dir die Lenden wie ein Mann, so will ich dich fragen, und du belehre mich!«
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
»Wo warst du, als ich die Erde baute? Sprich es aus, wenn du Einsicht besitzest!
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Wer hat ihre Maße bestimmt – du weißt es ja! –, oder wer hat die Meßschnur über sie ausgespannt?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Worauf sind ihre Grundpfeiler eingesenkt worden, oder wer hat ihren Eckstein gelegt,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
während die Morgensterne allesamt laut frohlockten und alle Gottessöhne jauchzten?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Und wer hat das Meer mit Toren verschlossen, als es hervorbrach, aus dem Mutterschoß heraustrat?
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
Als ich Gewölk zu seinem Kleide machte und dunkle Nebel zu seinen Windeln?
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
Als ich ihm das von mir bestimmte Gebiet absteckte und ihm Riegel und Tore herstellte
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
und sprach: ›Bis hierher darfst du kommen, aber nicht weiter, und hier soll sich der Stolz deiner Wellen brechen!‹
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Hast du jemals, seitdem du lebst, das Morgenlicht bestellt? Hast du dem Frührot seine Stätte angewiesen,
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
daß es die Säume der Erde erfasse und die Frevler von ihr verscheucht werden?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
Sie (die Erde) verwandelt sich alsdann wie Wachs unter dem Siegel, und alles stellt sich dar wie ein Prachtgewand;
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
den Frevlern aber wird ihr Licht entzogen, und der zum Schlagen schon erhobene Arm zerbricht.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Bist du bis zu den Quellen des Meeres gekommen, und hast du die tiefsten Tiefen des Weltmeers durchwandelt?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Haben sich vor dir die Pforten des Todes aufgetan, und hast du die Pforten des Schattenreichs gesehen?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Hast du die weiten Flächen der Erde überschaut? Sage an, wenn du dies alles weißt!
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Wo geht denn der Weg nach der Wohnung des Lichts, und die Finsternis, wo hat sie ihre Heimstätte,
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
daß du sie in ihr Gebiet hinbringen könntest und daß die Pfade zu ihrem Hause dir bekannt wären?
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Du weißt es ja, denn damals wurdest du ja geboren, und die Zahl deiner Lebenstage ist groß!
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Bist du zu den Vorratskammern des Schnees gekommen, und hast du die Speicher des Hagels gesehen,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
den ich aufgespart habe für die Drangsalszeiten, für den Tag des Kampfes und des Krieges?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Wo ist der Weg dahin, wo das Licht sich teilt und von wo der Ostwind sich über die Erde verbreitet?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Wer hat der Regenflut Kanäle gespalten und einen Weg dem Donnerstrahl gebahnt,
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
um regnen zu lassen auf menschenleeres Land, auf die Steppe, wo niemand wohnt,
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
um die Einöde und Wildnis reichlich zu tränken und Pflanzengrün sprießen zu lassen?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Hat der Regen einen Vater, oder wer erzeugt die Tropfen des Taues?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Aus wessen Mutterschoße geht das Eis hervor, und wer läßt den Reif des Himmels entstehen?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
Wie zu Stein verhärten sich die Wasser, und der Spiegel der Fluten schließt sich zur festen Decke zusammen.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Vermagst du die Bande des Siebengestirns zu knüpfen oder die Fesseln des Orion zu lösen?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Läßt du die Bilder des Tierkreises zur rechten Zeit hervortreten, und leitest du den Großen Bären samt seinen Jungen?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Kennst du die für den Himmel gültigen Gesetze, oder bestimmst du seine Herrschaft über die Erde?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Kannst du deine Stimme hoch zu den Wolken dringen lassen, daß strömender Regen dich bedecke?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Entsendest du die Blitze, daß sie hinfahren und zu dir sagen: ›Hier sind wir‹?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Wer hat Weisheit in die Wolkenschichten gelegt oder wer dem Luftgebilde Verstand verliehen?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Wer zählt die Federwolken mit Weisheit ab, und die Schläuche des Himmels, wer läßt sie sich ergießen,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
wenn das Erdreich sich zu Metallguß verhärtet hat und die Schollen sich fest zusammenballen?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Erjagst du für die Löwin die Beute, und stillst du die Gier der jungen Leuen,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
wenn sie in ihren Höhlen kauern, im Dickicht auf der Lauer liegen?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Wer verschafft dem Raben sein Futter, wenn seine Jungen zu Gott schreien und wegen Mangels an Nahrung umherirren?

< Ayuba 38 >