< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Und der HERR antwortete Hiob aus einem Wetter und sprach:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Wer ist der, der so fehlet in der Weisheit und redet so mit Unverstand?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Gürte deine Lenden wie ein Mann; ich will dich fragen, lehre mich!
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Wo warest du, da ich die Erde gründete? Sage mir's, bist du so klug?
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Weißt du, wer ihr das Maß gesetzt hat, oder wer über sie eine Richtschnur gezogen hat?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Oder worauf stehen ihre Füße versenket? Oder wer hat ihr einen Eckstein gelegt,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
da mich die Morgensterne miteinander lobeten, und jauchzeten alle Kinder Gottes?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Wer hat das Meer mit seinen Türen verschlossen, da es herausbrach wie aus Mutterleibe,
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
da ich's mit Wolken kleidete und in Dunkel einwickelte, wie in Windeln,
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
da ich ihm den Lauf brach mit meinem Damm und setzte ihm Riegel und Tür
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
und sprach: Bis hieher sollst du kommen und nicht weiter; hie sollen sich legen deine stolzen Wellen!?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Hast du bei deiner Zeit dem Morgen geboten und der Morgenröte ihren Ort gezeiget,
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
daß die Ecken der Erde gefasset und die Gottlosen herausgeschüttelt würden?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
Das Siegel wird sich wandeln wie Leimen, und sie stehen wie ein Kleid.
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
Und den Gottlosen wird ihr Licht genommen werden; und der Arm der Hoffärtigen wird zerbrochen werden.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Bist du in den Grund des Meers kommen und hast in den Fußtapfen der Tiefen gewandelt?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Haben sich dir des Todes Tore je aufgetan? Oder hast du gesehen die Tore der Finsternis?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Hast du vernommen, wie breit die Erde sei? Sage an, weißt du solches alles?
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Welches ist der Weg, da das Licht wohnet, und welches sei der Finsternis Stätte,
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
daß du mögest abnehmen seine Grenze und merken den Pfad zu seinem Hause?
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Wußtest du, daß du zu der Zeit solltest geboren werden und wieviel deiner Tage sein würden?
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Bist du gewesen, da der Schnee herkommt, oder hast du gesehen, wo der Hagel herkommt,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
die ich habe verhalten bis auf die Zeit der Trübsal und auf den Tag des Streits und Kriegs?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Durch welchen Weg teilet sich das Licht, und auffähret der Ostwind auf Erden?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Wer hat dem Platzregen seinen Lauf ausgeteilet und den Weg dem Blitze und Donner,
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
daß es regnet aufs Land, da niemand ist, in der Wüste, da kein Mensch ist,
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
daß er füllet die Einöden und Wildnis und macht, daß Gras wächset?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Wer ist des Regens Vater? Wer hat die Tropfen des Taues gezeuget?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Aus wes Leibe ist das Eis gegangen? Und wer hat den Reif unter dem Himmel gezeuget,
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
daß das Wasser verborgen wird wie unter Steinen und die Tiefe oben gestehet?
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Kannst du die Bande der sieben Sterne zusammenbinden, oder das Band des Orion auflösen?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Kannst du den Morgenstern hervorbringen zu seiner Zeit, oder den Wagen am Himmel über seine Kinder führen?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Weißt du, wie der Himmel zu regieren ist? Oder kannst du ihn meistern auf Erden?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Kannst du deinen Donner in der Wolke hoch herführen? Oder wird dich die Menge des Wassers verdecken?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Kannst du die Blitze auslassen, daß sie hinfahren und sprechen: Hie sind wir?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Wer gibt die Weisheit ins Verborgene? Wer gibt verständige Gedanken?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Wer ist so weise, der die Wolken erzählen könnte? Wer kann die Wasserschläuche am Himmel verstopfen,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
wenn der Staub begossen wird, daß er zuhaufe läuft und die Klöße aneinander kleben?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Kannst du der Löwin ihren Raub zu jagen geben und die jungen Löwen sättigen,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
daß sie sich legen in ihre Stätte und ruhen in der Höhle, da sie lauern?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Wer bereitet dem Raben die Speise, wenn seine Jungen zu Gott rufen und fliegen irre, wenn sie nicht zu essen haben?