< Ayuba 38 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Und Jehova antwortete Hiob aus dem Sturme und sprach:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Wer ist es, der den Rat verdunkelt mit Worten ohne Erkenntnis?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Gürte doch wie ein Mann deine Lenden; so will ich dich fragen, und du belehre mich!
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Wo warst du, als ich die Erde gründete? Tue es kund, wenn du Einsicht besitzest!
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Wer hat ihre Maße bestimmt, wenn du es weißt? Oder wer hat über sie die Meßschnur gezogen?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
In was wurden ihre Grundfesten eingesenkt?
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
Oder wer hat ihren Eckstein gelegt, als die Morgensterne miteinander jubelten und alle Söhne Gottes jauchzten?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Und wer hat das Meer mit Toren verschlossen, als es ausbrach, hervorkam aus dem Mutterschoße,
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
als ich Gewölk zu seinem Gewande und Wolkendunkel zu seiner Windel machte,
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
und ich ihm meine Grenze bestimmte und Riegel und Tore setzte,
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
und sprach: Bis hierher sollst du kommen und nicht weiter, und hier sei eine Schranke gesetzt dem Trotze deiner Wellen? -
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Hast du, seitdem du lebst, einem Morgen geboten? Hast du die Morgenröte ihre Stätte wissen lassen,
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
daß sie erfasse die Säume der Erde, und die Gesetzlosen von ihr verscheucht werden?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
Sie verwandelt sich wie Siegelton, und alles steht da wie in einem Gewande;
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
und den Gesetzlosen wird ihr Licht entzogen, und der erhobene Arm wird zerbrochen.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Bist du gekommen bis zu den Quellen des Meeres, und hast du die Gründe der Tiefe durchwandelt?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Wurden dir die Pforten des Todes enthüllt, und sahest du die Pforten des Todesschattens?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Hast du Einsicht genommen in die Breiten der Erde? Sage an, wenn du es alles weißt!
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Welches ist der Weg zur Wohnung des Lichtes, und die Finsternis, wo ist ihre Stätte?
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
Daß du sie hinbrächtest zu ihrer Grenze, und daß du der Pfade zu ihrem Hause kundig wärest.
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Du weißt es ja; denn damals wurdest du geboren, und die Zahl deiner Tage ist groß!
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Bist du zu den Vorräten des Schnees gekommen, und hast du gesehen die Vorräte des Hagels,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
die ich aufgespart habe für die Zeit der Bedrängnis, für den Tag des Kampfes und der Schlacht?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Welches ist der Weg, auf dem das Licht sich verteilt, der Ostwind sich verbreitet über die Erde?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Wer teilt der Regenflut Kanäle ab und einen Weg dem Donnerstrahle,
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
um regnen zu lassen auf ein Land ohne Menschen, auf die Wüste, in welcher kein Mensch ist,
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
um zu sättigen die Öde und Verödung, und um hervorsprießen zu lassen die Triebe des Grases?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Hat der Regen einen Vater, oder wer zeugt die Tropfen des Taues?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Aus wessen Schoße kommt das Eis hervor, und des Himmels Reif, wer gebiert ihn?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
Wie das Gestein verdichten sich die Wasser, und die Fläche der Tiefe schließt sich zusammen.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Kannst du knüpfen das Gebinde des Siebengestirns, oder lösen die Fesseln des Orion?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Kannst du die Bilder des Tierkreises hervortreten lassen zu ihrer Zeit, und den großen Bären leiten samt seinen Kindern?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Kennst du die Gesetze des Himmels, oder bestimmst du seine Herrschaft über die Erde?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Kannst du deine Stimme zum Gewölk erheben, daß eine Menge Wassers dich bedecke?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Kannst du Blitze entsenden, daß sie hinfahren, daß sie zu dir sagen: Hier sind wir? -
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Wer hat Weisheit in die Nieren gelegt, oder wer hat dem Geiste Verstand gegeben?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Wer zählt die Wolken mit Weisheit, und des Himmels Schläuche, wer gießt sie aus,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
wenn der Staub zu dichtem Gusse zusammenfließt und die Schollen aneinander kleben?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Erjagst du der Löwin den Raub, und stillst du die Gier der jungen Löwen,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
wenn sie in den Höhlen kauern, im Dickicht auf der Lauer sitzen?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Wer bereitet dem Raben seine Speise, wenn seine Jungen zu Gott schreien, umherirren ohne Nahrung?

< Ayuba 38 >