< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Or, répondant à Job du milieu d’un tourbillon, le Seigneur dit:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Quel est celui qui mêle des sentences à des discours maladroits?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Ceins tes reins comme un homme de cœur; je t’interrogerai, et réponds-moi.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Où étais-tu, quand je posais les fondements de la terre? Dis-le-moi, si tu as de l’intelligence.
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Qui a établi ses mesures, le sais-tu? ou qui a tendu sur elle le cordeau?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Sur quoi ses bases ont-elles été affermies? ou qui a posé sa pierre angulaire,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
Lorsque les astres du matin me louaient tous ensemble, et que tous les fils de Dieu étaient transportés de joie?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Qui a renfermé la mer dans des digues, quand elle s’élançait comme sortant d’un sein,
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
Lorsque je lui mettais un nuage pour vêtement, et que je l’enveloppais d’obscurité comme des langes de l’enfance?
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
Je l’ai environnée de mes limites, j’y ai mis un verrou et une porte à deux battants;
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
Et j’ai dit: Tu viendras jusque-là, et tu n’iras pas plus loin; et ici tu briseras tes flots orgueilleux.
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Est-ce que depuis ta naissance tu as commandé à l’étoile du matin, et tu as montré à l’aurore son lieu?
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
Et as-tu tenu, en les ébranlant, les extrémités de la terre, et en as-tu chassé les impies?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
Elle sera rétablie comme une terre molle de cachet, et elle demeurera comme un vêtement.
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
La lumière des impies leur sera ôté, et leur bras élevé sera brisé.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Est-ce que tu es entré dans les profondeurs de la mer, et as-tu marché dans les extrémités de l’abîme?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Est-ce que les portes de la mort ont été ouvertes pour toi? et les portes ténébreuses, les as-tu vues?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Est-ce que tu as considéré l’étendue de la terre? Enseigne-moi, si tu les connais, toutes ces choses;
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
En quelle voie la lumière habite, et quel est le lieu des ténèbres;
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
En sorte que tu conduises chacune d’elles à son terme, et que tu connaisses les sentiers de leur demeure.
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Car savais-tu alors que tu devais naître? et le nombre de tes jours, l’avais-tu connu?
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Est-ce que tu es entré dans les trésors de la neige, ou as-tu aperçu les trésors de la grêle,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
Que j’ai préparées pour le temps de l’ennemi, pour le jour de la guerre et du combat?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Sais-tu par quelle voie se répand la lumière, et se distribue la chaleur sur la terre?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Qui a donné cours à l’ondée la plus impétueuse, et une voie au tonnerre éclatant,
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
Pour faire pleuvoir sur une terre sans homme dans un désert, où aucun des mortels ne demeure,
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
Pour inonder une terre inaccessible et désolée, et y produire des herbes vertes?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Qui est le père de la pluie? ou qui a engendré les gouttes de la rosée?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Du sein de qui est sortie la glace? et la gelée du ciel, qui l’a engendrée?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
À la manière de la pierre les eaux se durcissent, et la surface de l’abîme devient solide.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Est-ce que tu seras capable de joindre ensemble les brillantes étoiles des Pléiades, ou pourrastu interrompre le cours d’Arcturus?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Est-ce que tu produis Lucifer en son temps, et que tu fais lever l’étoile du soir sur les fils de la terre?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Est-ce que tu connais l’ordre du ciel, et en rendras-tu raison sur la terre?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Est-ce que tu élèveras ta voix dans les nuages, et que l’impétuosité des eaux te couvrira?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Est-ce que tu enverras les foudres, et elles iront; et, revenant, te diront-elles: Nous voici?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Qui a mis au dedans de l’homme la sagesse? ou qui a donné au coq l’intelligence?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Qui expliquera la conduite des cieux, et qui fera cesser le concert du ciel?
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
Quand la poussière se répandait-elle sur la terre, et les glèbes se durcissaient-elles?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Est-ce que tu prendras la proie pour la lionne, et empliras-tu l’âme de ses petits,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
Quand ils sont couchés dans leurs antres, et qu’ils épient dans leurs cavernes?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Qui prépare au corbeau sa nourriture, quand ses petits crient à Dieu, errant ça et là, parce qu’ils n’ont rien à manger?