< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Et l'Éternel répondit à Job du milieu de la tempête et dit:
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Qui est-ce qui obscurcit mes décrets par des discours dénués d'intelligence?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Eh bien! ceins tes reins, comme un homme! puis je te questionnerai, et tu m'instruiras.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Où étais-tu, quand je fondai la terre? Indique-le, si tu as vraiment la science!
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Qui est-ce qui en fixa la dimension, que tu saches, ou étendit sur elle le cordeau?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Quel est le support jusqu'où ses bases plongent? Ou qui est-ce qui en a posé la pierre angulaire,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
aux accords unanimes des étoiles du matin, aux acclamations de tous les Fils de Dieu?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Et qui est-ce qui enferma la mer entre des portes, quand elle fit éruption du sein maternel;
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
quand je lui donnai la nuée pour manteau, et les sombres vapeurs pour lui servir de langes;
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
quand je lui prescrivis ma loi, et que j'établis ses barres et ses portes,
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
et que je dis: Jusqu'ici tu viendras, et pas plus avant! et ici s'arrêtera l'orgueil de tes vagues?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
De ton vivant as-tu commandé au matin, et fait connaître à l'aurore le lieu d'où elle part,
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
pour saisir la terre par ses bords? Alors les impies en sont balayés,
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
alors la terre prend une face nouvelle, telle que l'argile qui reçoit une empreinte, et toutes choses paraissent comme pour la vêtir;
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
alors les impies perdent la clarté qu'ils aiment, et le bras qu'ils ont levé déjà, se brise.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
As-tu pénétré jusqu'aux sources des mers, et au fond de l'abîme as-tu porté tes pas?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Les portes de la mort te furent-elles découvertes? As-tu vu les portes de la sombre mort?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Ton regard embrasse-t-il les contours de la terre? Raconte, si tu sais toutes ces choses!
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Quelle route mène où la lumière habite? et la nuit, où fait-elle son séjour?
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
Iras-tu les chercher l'une et l'autre, pour les amener chacune à leurs limites? Et connais-tu le chemin de leur demeure?
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Tu le sais! car alors tu étais déjà né! et le nombre de tes jours est immense!
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
As-tu pénétré jusqu'aux dépôts de la neige, et as-tu vu les dépôts de la grêle,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
que je réserve pour les temps du désastre, pour le jour du combat et de la bataille?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Quel chemin mène aux lieux où la lumière se divise, d'où le vent d'Est se répand sur la terre?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Qui a fait ces conduits qui éparpillent la pluie, et a tracé une route à la foudre bruyante,
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
afin d'arroser une terre inhabitée, une steppe où il n'y a pas un humain,
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
afin d'abreuver les lieux déserts et solitaires, et de fertiliser le sol qui donne le gazon?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
La pluie a-t-elle un père? Ou qui est-ce qui engendra les gouttes de la rosée?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Du sein de qui la glace sort-elle? et qui est-ce qui produit le givre du ciel?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
Comme la pierre, les eaux se condensent, et la surface de l'abîme est enchaînée.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
As-tu formé le lien qui unit les Pléiades? Ou peux-tu détacher les chaînes d'Orion?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Fais-tu paraître en leur temps les signes du Zodiaque? Ou conduis-tu Arcture avec son cortège?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Connais-tu les lois des Cieux? Les as-tu mis à même d'influer sur la terre?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Parles-tu à la nue avec autorité, et te couvre-t-elle aussitôt d'une eau abondante?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Lances-tu des foudres, et partent-elles, et disent-elles: Nous voici?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Qui a mis une sagesse dans les sombres nuages, et a donné aux météores une intelligence?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Qui a calculé les nuées avec sagesse? Et qui est-ce qui incline les urnes des Cieux,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
quand la poussière coule comme un métal en fonte, et que les glèbes se collent l'une à l'autre?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Pour la lionne vas-tu chasser une proie? et assouvis-tu la faim des lionceaux,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
quand ils sont blottis dans leurs repaires, ou dans leurs tanières, tapis en embuscade?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Qui est-ce qui procure au corbeau sa pâture, quand ses petits poussent vers Dieu leurs cris, et errent affamés?