< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
And Jehovah answereth Job out of the whirlwind, and saith: —
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Who [is] this — darkening counsel, By words without knowledge?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Gird, I pray thee, as a man, thy loins, And I ask thee, and cause thou Me to know.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Where wast thou when I founded earth? Declare, if thou hast known understanding.
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Who placed its measures — if thou knowest? Or who hath stretched out upon it a line?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
On what have its sockets been sunk? Or who hath cast its corner-stone?
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
In the singing together of stars of morning, And all sons of God shout for joy,
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
And He shutteth up with doors the sea, In its coming forth, from the womb it goeth out.
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
In My making a cloud its clothing, And thick darkness its swaddling band,
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
And I measure over it My statute, And place bar and doors,
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
And say, 'Hitherto come thou, and add not, And a command is placed On the pride of thy billows.'
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Hast thou commanded morning since thy days? Causest thou the dawn to know its place?
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
To take hold on the skirts of the earth, And the wicked are shaken out of it,
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
It turneth itself as clay of a seal And they station themselves as clothed.
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
And withheld from the wicked is their light, And the arm lifted up is broken.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Hast thou come in to springs of the sea? And in searching the deep Hast thou walked up and down?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Revealed to thee were the gates of death? And the gates of death-shade dost thou see?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Thou hast understanding, Even unto the broad places of earth! Declare — if thou hast known it all.
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Where [is] this — the way light dwelleth? And darkness, where [is] this — its place?
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
That thou dost take it unto its boundary, And that thou dost understand The paths of its house.
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Thou hast known — for then thou art born And the number of thy days [are] many!
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Hast thou come in unto the treasure of snow? Yea, the treasures of hail dost thou see?
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
That I have kept back for a time of distress, For a day of conflict and battle.
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Where [is] this, the way light is apportioned? It scattereth an east wind over the earth.
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Who hath divided for the flood a conduit? And a way for the lightning of the voices?
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
To cause [it] to rain on a land — no man, A wilderness — no man in it.
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
To satisfy a desolate and waste place, And to cause to shoot up The produce of the tender grass?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Hath the rain a father? Or who hath begotten the drops of dew?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
From whose belly came forth the ice? And the hoar-frost of the heavens, Who hath begotten it?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
As a stone waters are hidden, And the face of the deep is captured.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Dost thou bind sweet influences of Kimah? Or the attractions of Kesil dost thou open?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Dost thou bring out Mazzaroth in its season? And Aysh for her sons dost thou comfort?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Hast thou known the statutes of heaven? Or dost thou appoint Its dominion in the earth?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Dost thou lift up to the cloud thy voice, And abundance of water doth cover thee?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Dost thou send out lightnings, and they go And say unto thee, 'Behold us?'
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Who hath put in the inward parts wisdom? Or who hath given To the covered part understanding?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Who doth number the clouds by wisdom? And the bottles of the heavens, Who doth cause to lie down,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
In the hardening of dust into hardness, And clods cleave together?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Dost thou hunt for a lion prey? And the desire of young lions fulfil?
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
When they bow down in dens — Abide in a thicket for a covert?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Who doth prepare for a raven his provision, When his young ones cry unto God? They wander without food.