< Ayuba 38 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Then Yahweh responded to Job, out of a storm, and said: —
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Who is it that darkeneth counsel, by words, without knowledge?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Gird, I pray thee—like a strong man—thy loins, that I may ask thee, and inform thou me:
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Where wast thou, when I founded the earth? Tell, if thou knowest understanding!
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Who set the measurements thereof, if thou knowest? Or who stretched out over it a line?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Whereon were the pedestals thereof sunk? Or who laid the corner stone thereof; —
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
When the morning stars sang together, and all the sons of God shouted for joy?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Or [who] shut in, with double doors, the sea, when, bursting out of the womb, it came forth;
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
When I put a cloud as the garment thereof, and a thick cloud as the swaddling-band thereof;
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
And brake off for it my boundary, and fixed a bar and double doors;
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
And said—Hitherto, shalt thou come, and no further, —and, here, shalt thou set a limit to the majesty of thy waves?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Since thy days [began] hast thou commanded the morning? or caused the dawn to know its place;
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
That it might lay hold of the wings of the earth, and the lawless be shaken out of it?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
It transformeth itself like the clay of a seal, so that things stand forth like one arrayed;
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
That their light may be withdrawn from the lawless, and, the lofty arm, be shivered.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Hast thou entered as far as the springs of the sea? Or, through the secret recesses of the resounding deep, hast thou wandered?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Have the gates of death been disclosed to thee? And, the gates of the death-shade, couldst thou descry?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Hast thou well considered, even the breadths of the earth? Tell—if thou knowest it all!
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Where then is the way, the light shall abide? And, the darkness, where then is its place?
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
That thou mayest conduct it unto the bound thereof, and that thou mayest perceive the paths to its house.
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Thou knowest, for, then, hadst thou been born! And, in number, thy days are many!
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Hast thou entered into the treasuries of the snow? And, the treasuries of the hail, couldst thou see?
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
Which I have reserved for a time of distress, for the day of conflict and of war?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Where then is the way the lightning is parted? The east wind spreadeth itself abroad over the earth.
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Who hath cloven—for the torrent—a channel? Or a way for the lightning of thunders;
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
To give rain over the no-man’s land, the desert, where no son of earth is;
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
To satisfy the wild and the wilderness, to cause to spring forth the meadow of young grass?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Hath the rain a father? Or who hath begotten the drops of dew?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Out of whose womb, came forth the ice? And, the hoar-frost of the heavens, who hath given it birth?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
Like a stone, are the waters congealed, and, the face of the roaring deep, becometh firm!
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Canst thou bind the fetters of the Pleiades? Or, the bands of Orion, canst thou unloose?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Canst thou bring forth the signs of the Zodiac each in its season? Or, the Bear and her Young, canst thou lead?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Knowest thou, the statutes of the heavens? Or didst thou appoint his dominion over the earth?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Canst thou lift up, to the thick cloud, thy voice, and the overflow of waters cover thee?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Canst thou send forth the lightnings, so that they go, and say to thee, Behold us?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Who hath put—into cloud-forms—wisdom? Or who hath given—to the meteor—understanding?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Who can count the thin clouds, in wisdom? And, the bottles of the heavens, who can empty out;
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
When the dust is cast into a clod, and the lumps are bound together?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Wilt thou hunt—for the Lioness—prey? Or, the craving of the Strong Lion, wilt thou satisfy;
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
When they settle down in dens, abide in covert, for lying in wait?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Who prepareth for the Raven his nourishment, —when his young ones—unto GOD—cry out, [when] they wander for lack of food?

< Ayuba 38 >