< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
Then YHWH answered Job out of the whirlwind, and said,
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Who is this that darkeneth counsel by words without knowledge?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Gird up now thy loins like a man; for I will demand of thee, and answer thou me.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Where wast thou when I laid the foundations of the earth? declare, if thou hast understanding.
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
Who hath laid the measures thereof, if thou knowest? or who hath stretched the line upon it?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
Whereupon are the foundations thereof fastened? or who laid the corner stone thereof;
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
When the morning stars sang together, and all the sons of Elohim shouted for joy?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Or who shut up the sea with doors, when it brake forth, as if it had issued out of the womb?
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
When I made the cloud the garment thereof, and thick darkness a swaddlingband for it,
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
And brake up for it my decreed place, and set bars and doors,
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
And said, Hitherto shalt thou come, but no further: and here shall thy proud waves be stayed?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Hast thou commanded the morning since thy days; and caused the dayspring to know his place;
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
That it might take hold of the ends of the earth, that the wicked might be shaken out of it?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
It is turned as clay to the seal; and they stand as a garment.
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
And from the wicked their light is withholden, and the high arm shall be broken.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Hast thou entered into the springs of the sea? or hast thou walked in the search of the depth?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Have the gates of death been opened unto thee? or hast thou seen the doors of the shadow of death?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Hast thou perceived the breadth of the earth? declare if thou knowest it all.
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Where is the way where light dwelleth? and as for darkness, where is the place thereof,
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
That thou shouldest take it to the bound thereof, and that thou shouldest know the paths to the house thereof?
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
Knowest thou it, because thou wast then born? or because the number of thy days is great?
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Hast thou entered into the treasures of the snow? or hast thou seen the treasures of the hail,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
Which I have reserved against the time of trouble, against the day of battle and war?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
By what way is the light parted, which scattereth the east wind upon the earth?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
Who hath divided a watercourse for the overflowing of waters, or a way for the lightning of thunder;
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
To cause it to rain on the earth, where no man is; on the wilderness, wherein there is no man;
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
To satisfy the desolate and waste ground; and to cause the bud of the tender herb to spring forth?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Hath the rain a father? or who hath begotten the drops of dew?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Out of whose womb came the ice? and the hoary frost of heaven, who hath gendered it?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
The waters are hid as with a stone, and the face of the deep is frozen.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Canst thou bind the sweet influences of Pleiades, or loose the bands of Orion?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Canst thou bring forth Mazzaroth in his season? or canst thou guide Arcturus with his sons?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Knowest thou the ordinances of heaven? canst thou set the dominion thereof in the earth?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Canst thou lift up thy voice to the clouds, that abundance of waters may cover thee?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Canst thou send lightnings, that they may go, and say unto thee, Here we are?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Who hath put wisdom in the inward parts? or who hath given understanding to the heart?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
Who can number the clouds in wisdom? or who can stay the bottles of heaven,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
When the dust groweth into hardness, and the clods cleave fast together?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Wilt thou hunt the prey for the lion? or fill the appetite of the young lions,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
When they couch in their dens, and abide in the covert to lie in wait?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Who provideth for the raven his food? when his young ones cry unto El, they wander for lack of meat.