< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
And the Lord made answer to Job out of the storm-wind, and said,
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
Who is this who makes the purpose of God dark by words without knowledge?
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
Get your strength together like a man of war; I will put questions to you, and you will give me the answers.
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
Where were you when I put the earth on its base? Say, if you have knowledge.
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
By whom were its measures fixed? Say, if you have wisdom; or by whom was the line stretched out over it?
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
On what were its pillars based, or who put down its angle-stone,
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
When the morning stars made songs together, and all the sons of the gods gave cries of joy?
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
Or where were you when the sea came to birth, pushing out from its secret place;
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
When I made the cloud its robe, and put thick clouds as bands round it,
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
Ordering a fixed limit for it, with locks and doors;
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
And said, So far you may come, and no farther; and here the pride of your waves will be stopped?
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
Have you, from your earliest days, given orders to the morning, or made the dawn conscious of its place;
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
So that it might take a grip of the skirts of the earth, shaking all the evil-doers out of it?
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
It is changed like wet earth under a stamp, and is coloured like a robe;
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
And from the evil-doers their light is kept back, and the arm of pride is broken.
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
Have you come into the springs of the sea, walking in the secret places of the deep?
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
Have the doors of death been open to you, or have the door-keepers of the dark ever seen you?
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Have you taken note of the wide limits of the earth? Say, if you have knowledge of it all.
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
Which is the way to the resting-place of the light, and where is the store-house of the dark;
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
So that you might take it to its limit, guiding it to its house?
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
No doubt you have knowledge of it, for then you had come to birth, and the number of your days is great.
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
Have you come into the secret place of snow, or have you seen the store-houses of the ice-drops,
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
Which I have kept for the time of trouble, for the day of war and fighting?
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
Which is the way to the place where the wind is measured out, and the east wind sent out over the earth?
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
By whom has the way been cut for the flowing of the rain, and the flaming of the thunder;
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
Causing rain to come on a land where no man is living, on the waste land which has no people;
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
To give water to the land where there is waste and destruction, and to make the dry land green with young grass?
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
Has the rain a father? or who gave birth to the drops of night mist?
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
Out of whose body came the ice? and who gave birth to the cold mist of heaven?
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
The waters are joined together, hard as a stone, and the face of the deep is covered.
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
Are the bands of the Pleiades fixed by you, or are the cords of Orion made loose?
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
Do you make Mazzaroth come out in its right time, or are the Bear and its children guided by you?
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
Have you knowledge of the laws of the heavens? did you give them rule over the earth?
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
Is your voice sent up to the cloud, so that you may be covered by the weight of waters?
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
Do you send out the thunder-flames, so that they may go, and say to you, Here we are?
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
Who has put wisdom in the high clouds, or given knowledge to the lights of the north?
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
By whose wisdom are the clouds numbered, or the water-skins of the heavens turned to the earth,
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
When the earth becomes hard as metal, and is joined together in masses?
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
Do you go after food for the she-lion, or get meat so that the young lions may have enough,
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
When they are stretched out in their holes, and are waiting in the brushwood?
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Who gives in the evening the meat he is searching for, when his young ones are crying to God; when the young lions with loud noise go wandering after their food?