< Ayuba 37 >
1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
A ESTO también se espanta mi corazón, y salta de su lugar.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Oid atentamente su voz terrible, y el sonido que sale de su boca.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Debajo de todos los cielos lo dirige, y su luz hasta los fines de la tierra.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
Después de ella bramará el sonido, tronará él con la voz de su magnificencia; y aunque sea oída su voz, no los detiene.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Tronará Dios maravillosamente con su voz; él hace grandes cosas, que nosotros no entendemos.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Porque á la nieve dice: Desciende á la tierra; también á la llovizna, y á los aguaceros de su fortaleza.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Así hace retirarse á todo hombre, para que los hombres todos reconozcan su obra.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
La bestia se entrará en su escondrijo, y estaráse en sus moradas.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Del mediodía viene el torbellino, y el frío de los vientos del norte.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
Por el soplo de Dios se da el hielo, y las anchas aguas son constreñidas.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Regando también llega á disipar la densa nube, y con su luz esparce la niebla.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
Asimismo por sus designios se revuelven las nubes en derredor, para hacer sobre la haz del mundo, en la tierra, lo que él les mandara.
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Unas veces por azote, otras por causa de su tierra, otras por misericordia las hará parecer.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Escucha esto, Job; repósate, y considera las maravillas de Dios.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
¿Supiste tú cuándo Dios las ponía en concierto, y hacía levantar la luz de su nube?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
¿Has tú conocido las diferencias de las nubes, las maravillas del Perfecto en sabiduría?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
¿Por qué están calientes tus vestidos cuando se fija el [viento del] mediodía sobre la tierra?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
¿Extendiste tú con él los cielos, firmes como un espejo sólido?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Muéstranos qué le hemos de decir; [porque] nosotros no podemos componer [las ideas] á causa de las tinieblas.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
¿Será preciso contarle cuando yo hablaré? Por más que el hombre razone, quedará como abismado.
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
He aquí aún: no se puede mirar la luz esplendente en los cielos, luego que pasa el viento y los limpia,
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Viniendo de la parte del norte la dorada claridad. En Dios hay una majestad terrible.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
El [es] Todopoderoso, al cual no alcanzamos, grande en potencia; y en juicio y en multitud de justicia no afligirá.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Temerlo han por tanto los hombres: él no mira á los sabios de corazón.