< Ayuba 37 >
1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
A esto también se espanta mi corazón y salta de su lugar.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Oíd oyendo su terrible voz, y la palabra que sale de su boca.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Debajo de todos los cielos lo enderezará, y su luz le extenderá hasta los fines de la tierra.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
Tras de él bramará el sonido, tronará con su valiente voz, y aunque sea oída su voz, no los detiene.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Tronará Dios maravillosamente con su voz: él hace grandes cosas, y nosotros no lo entendemos.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Porque a la nieve dice: Sé en la tierra; y lluvia tras lluvia, y lluvia tras lluvia en su fortaleza.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Él pone un sello en la mano de todos los hombres, para que todos los hombres conozcan su obra.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
La bestia se entrará en su escondrijo, y habitará en sus moradas.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Del mediodía viene el torbellino, y de los vientos del norte el frío.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
Por el soplo de Dios se da el hielo, y las anchas aguas son constreñidas.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Además de esto, con la claridad fatiga las nubes, y las esparce con su luz.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
Y ellas se revuelven al derredor por sus ingenios, para hacer sobre la haz del mundo en la tierra lo que él les mandó:
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Unas veces por azote; otras, por causa de su tierra; otras, por misericordia las hará parecer.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Escucha esto Job, repósate, y considera las maravillas de Dios.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
¿Supiste tú cuando Dios las ponía en concierto, y hacía levantar la luz de su nube?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
¿Has tú conocido las diferencias de las nubes, las maravillas del perfecto de sabidurías?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
¿Y eran calientes tus vestidos cuando él daba el reposo a la tierra del mediodía?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
¿Extendiste tú con él los cielos firmes, como un espejo firme?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Muéstranos, que le hemos de decir, porque no ordenemos en tinieblas.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
¿Ha de serle contado cuando yo hablare? ¿Ha de serle dicho cuando alguno será damnificado?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
También alguna vez no se ve la luz clara en los cielos; y pasa un viento y límpialos.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
De la parte del norte vendrá la serenidad, por el Dios terrible de alabanza.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
Él es Todopoderoso, al cual no alcanzamos: grande en poder, y en juicio, y en multitud de justicia; no aflige.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Por tanto los hombres le temerán, todos los sabios de corazón no le comprenderán.