< Ayuba 37 >
1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
“Sí, ante esto mi corazón tiembla, y es desplazado de su lugar.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Escucha, oh, escucha el ruido de su voz, el sonido que sale de su boca.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Lo envía bajo todo el cielo, y sus rayos hasta los confines de la tierra.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
Tras ella ruge una voz. Truena con la voz de su majestad. No se guarda nada cuando se escucha su voz.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Dios truena maravillosamente con su voz. Él hace grandes cosas, que no podemos comprender.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Porque dice a la nieve: “Cae sobre la tierra”. también a la lluvia, y a los chubascos de su poderosa lluvia.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Él sella la mano de cada hombre, para que todos los hombres a los que ha hecho lo conozcan.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Entonces los animales se ponen a cubierto, y permanecen en sus guaridas.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
De su habitación sale la tormenta, y el frío del norte.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
Por el soplo de Dios se da el hielo, y la anchura de las aguas está congelada.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Sí, carga la espesa nube con humedad. Extiende la nube de su rayo.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
Se ha dado la vuelta gracias a su guía, para que hagan todo lo que él les mande en la superficie del mundo habitable,
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
ya sea por la corrección, o por su tierra, o por la bondad amorosa, que la hace venir.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
“Escucha esto, Job. Quédate quieto y considera las obras maravillosas de Dios.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
¿Sabes cómo los controla Dios? y hace brillar el rayo de su nube?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
¿Conoces el funcionamiento de las nubes, las obras maravillosas de aquel que es perfecto en el conocimiento?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
Tú, cuya ropa es cálida cuando la tierra está quieta a causa del viento del sur?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
¿Puedes, con él, extender el cielo, que es fuerte como un espejo de metal fundido?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Enséñanos lo que le vamos a decir, porque no podemos hacer nuestro caso a causa de la oscuridad.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
¿Se le dirá que voy a hablar? ¿O debería un hombre desear ser tragado?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Los hombres no ven la luz que brilla en los cielos, pero el viento pasa y los despeja.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Del norte viene el esplendor dorado. Con Dios hay una majestuosidad impresionante.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
No podemos llegar al Todopoderoso. Está exaltado en el poder. Con justicia y gran rectitud, no oprimirá.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Por eso los hombres lo veneran. No tiene en cuenta a los sabios de corazón”.