< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
“Ante esto mi corazón tiembla, latiendo rápidamente dentro de mí.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Escucha con atención la voz atronadora de Dios que retumba al hablar.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Lo envía a través del cielo; sus relámpagos brillan hasta los confines de la tierra.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
Luego viene el estruendo del trueno, su voz majestuosa no se contiene cuando habla.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
¡La voz atronadora de Dios es maravillosa! No podemos comprender las grandes cosas que hace.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
“Ordena que caiga la nieve y que llueva sobre la tierra.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Con ello detiene el trabajo de la gente para que todos puedan entender lo que hace.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Incluso los animales se refugian y permanecen en sus guaridas.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
El viento del sur sopla en las tormentas, mientras que el viento del norte sopla cuando hace frío.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
El aliento de Dios produce hielo, congelando la superficie del agua.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Llena las nubes de humedad y esparce desde ellas sus rayos.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
Se arremolinan bajo su control; se mueven por toda la tierra según sus órdenes.
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Lo hace para cumplir su voluntad, ya sea para disciplinar o para mostrar su bondad.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
“Escucha esto, Job. Detente un momento y considera las cosas maravillosas que hace Dios.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
¿Sabes cómo Dios controla las nubes, o cómo hace que sus relámpagos salgan de ellas?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
¿Sabes cómo flotan las nubes en el cielo: la maravillosa obra de quien lo sabe todo.
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
Tú sabes que tu ropa gotea de sudor cuando el viento del sur trae un aire caliente y pesado.
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
¿Puedes martillar el cielo para que sea como un espejo fundido, como hace él?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
“Entonces, ¿por qué no nos enseñas lo que hay que decirle a Dios? No podemos exponer nuestro caso porque estamos a oscuras!
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
¿Hay que decirle a Dios que quiero hablar? Cualquiera que lo quisiera sería destruido!
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Al fin y al cabo, no podemos mirar al sol cuando brilla en el cielo, después de que el viento haya despejado las nubes.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Del norte sale Dios brillando como el oro, rodeado de una majestad impresionante.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
No podemos acercarnos al Todopoderoso, porque nos supera en poder y justicia, y en hacer el bien.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
No actúa como un tirano; no es de extrañar que la gente le tema, aunque no valora a los que se creen sabios”.

< Ayuba 37 >