< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
super hoc expavit cor meum et emotum est de loco suo
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
audite auditionem in terrore vocis eius et sonum de ore illius procedentem
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
subter omnes caelos ipse considerat et lumen illius super terminos terrae
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
post eum rugiet sonitus tonabit voce magnitudinis suae et non investigabitur cum audita fuerit vox eius
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
tonabit Deus in voce sua mirabiliter qui facit magna et inscrutabilia
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
qui praecipit nivi ut descendat in terram et hiemis pluviis et imbri fortitudinis suae
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
qui in manu omnium hominum signat ut noverint singuli opera sua
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
ingredietur bestia latibulum et in antro suo morabitur
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
ab interioribus egreditur tempestas et ab Arcturo frigus
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
flante Deo concrescit gelu et rursum latissimae funduntur aquae
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
frumentum desiderat nubes et nubes spargunt lumen suum
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
quae lustrant per circuitum quocumque eas voluntas gubernantis duxerit ad omne quod praeceperit illis super faciem orbis terrarum
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
sive in una tribu sive in terra sua sive in quocumque loco misericordiae suae eas iusserit inveniri
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
ausculta haec Iob sta et considera miracula Dei
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
numquid scis quando praeceperit Deus pluviis ut ostenderent lucem nubium eius
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
numquid nosti semitas nubium magnas et perfectas scientias
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
nonne vestimenta tua calida sunt cum perflata fuerit terra austro
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
tu forsitan cum eo fabricatus es caelos qui solidissimi quasi aere fusi sunt
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
ostende nobis quid dicamus illi nos quippe involvimur tenebris
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
quis narrabit ei quae loquor etiam si locutus fuerit homo devorabitur
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
at nunc non vident lucem subito aer cogitur in nubes et ventus transiens fugabit eas
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
ab aquilone aurum venit et ad Deum formidolosa laudatio
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
digne eum invenire non possumus magnus fortitudine et iudicio et iustitia et enarrari non potest
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
ideo timebunt eum viri et non audebunt contemplari omnes qui sibi videntur esse sapientes

< Ayuba 37 >