< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
Per questo mi batte forte il cuore e mi balza fuori dal petto.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Udite, udite, il rumore della sua voce, il fragore che esce dalla sua bocca.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Il lampo si diffonde sotto tutto il cielo e il suo bagliore giunge ai lembi della terra;
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
dietro di esso brontola il tuono, mugghia con il suo fragore maestoso e nulla arresta i fulmini, da quando si è udita la sua voce;
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
mirabilmente tuona Dio con la sua voce opera meraviglie che non comprendiamo!
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Egli infatti dice alla neve: «Cadi sulla terra» e alle piogge dirotte: «Siate violente».
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Rinchiude ogni uomo in casa sotto sigillo, perché tutti riconoscano la sua opera.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Le fiere si ritirano nei loro ripari e nelle loro tane si accovacciano.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Dal mezzogiorno avanza l'uragano e il freddo dal settentrione.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
Al soffio di Dio si forma il ghiaccio e la distesa dell'acqua si congela.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Carica di umidità le nuvole e le nubi ne diffondono le folgori.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
Egli le fa vagare dappertutto secondo i suoi ordini, perché eseguiscano quanto comanda loro sul mondo intero.
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Le manda o per castigo della terra o in segno di bontà.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Porgi l'orecchio a questo, Giobbe, soffèrmati e considera le meraviglie di Dio.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
Sai tu come Dio le diriga e come la sua nube produca il lampo?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Conosci tu come la nube si libri in aria, i prodigi di colui che tutto sa?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
Come le tue vesti siano calde quando non soffia l'austro e la terra riposa?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
Hai tu forse disteso con lui il firmamento, solido come specchio di metallo fuso?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Insegnaci che cosa dobbiamo dirgli. Noi non parleremo per l'oscurità.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Gli si può forse ordinare: «Parlerò io?». O un uomo può dire che è sopraffatto?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Ora diventa invisibile la luce, oscurata in mezzo alle nubi: ma tira il vento e le spazza via.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Dal nord giunge un aureo chiarore, intorno a Dio è tremenda maestà.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
L’Onnipotente noi non lo possiamo raggiungere, sublime in potenza e rettitudine e grande per giustizia: egli non ha da rispondere.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Perciò gli uomini lo temono: a lui la venerazione di tutti i saggi di mente.

< Ayuba 37 >