< Ayuba 37 >
1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
Des entsetzt sich mein Herz und bebet.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Lieber, höret doch, wie sein Donner zürnet, und was für Gespräch von seinem Munde ausgehet!
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Er siehet unter allen Himmeln, und sein Blitz scheinet auf die Enden der Erde.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
Dem nach brüllet der Donner, und er donnert mit seinem großen Schall, und wenn sein Donner gehöret wird, kann man's nicht aufhalten.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Gott donnert mit seinem Donner greulich und tut große Dinge, und wird doch nicht erkannt.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Er spricht zum Schnee, so ist er bald auf Erden, und zum Platzregen, so ist der Platzregen da mit Macht.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Alle Menschen hat er in der Hand als verschlossen, daß die Leute lernen, was er tun kann.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Das wilde Tier gehet in die Höhle und bleibt an seinem Ort.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Von Mittag her kommt Wetter und von Mitternacht Kälte.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
Vom Odem Gottes kommt Frost, und große Wasser, wenn er auftauen läßt.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Die dicken Wolken scheiden sich, daß es helle werde, und durch den Nebel bricht sein Licht.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
Er kehret die Wolken, wo er hin will, daß sie schaffen alles, was er ihnen gebeut, auf dem Erdboden,
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
es sei über ein Geschlecht oder über ein Land, so man ihn barmherzig findet.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Da merke auf, Hiob; stehe, und vernimm die Wunder Gottes!
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
Weißt du, wenn Gott solches über sie bringt und wenn er das Licht seiner Wolken läßt hervorbrechen?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Weißt du, wie sich die Wolken ausstreuen? Welche Wunder die Vollkommenen wissen.
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
Daß deine Kleider warm sind, wenn das Land stille ist vom Mittagswind?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
Ja, du wirst mit ihm die Wolken ausbreiten, die fest stehen wie ein gegossener Spiegel.
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Zeige uns, was wir ihm sagen sollen; denn wir werden nicht dahin reichen vor Finsternis.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Wer wird ihm erzählen, daß ich rede? So jemand redet, der wird verschlungen.
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Jetzt siehet man das Licht nicht, das in den Wolken helle leuchtet; wenn aber der Wind wehet, so wird's klar.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Von Mitternacht kommt Gold zu Lob vor dem schrecklichen Gott.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
Den Allmächtigen aber mögen sie nicht begreifen, der so groß ist von Kraft; denn er wird von seinem Recht und guter Sache nicht Rechenschaft geben.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Darum müssen ihn fürchten die Leute; und er fürchtet sich vor keinem, wie weise sie sind.