< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
C’Est aussi ce qui jette la frayeur dans mon cœur et le fait vivement tressauter.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Ecoutez attentivement le grondement de sa voix et le roulement qui sort de sa bouche.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Il le prolonge sous toute la voûte des cieux, et ses éclairs brillent jusqu’aux extrémités de la terre.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
A leur suite, c’est un bruit qui rugit: il tonne de sa voix majestueuse, et quand cette voix se fait entendre, il ne les retient plus.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Dieu fait retentir merveilleusement la voix de son tonnerre; il accomplit de grandes choses qui dépassent notre connaissance.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Car il dit à la neige: "Apparais sur la terre!" II envoie la pluie abondante, ses puissantes averses.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Alors il paralyse les bras de tous les hommes, afin que ces hommes, son œuvre à lui, apprennent à le connaître.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Et les fauves rentrent dans leur tanière et se terrent dans leur gîte.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
L’Ouragan surgit de ses retraites, le froid est amené par les vents d’aquilon.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
Au souffle de Dieu se forme la glace et se contractent les nappes d’eau.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Il charge aussi la nue de vapeurs humides, dissémine ses nuages que traversent les éclairs.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
Et ces nuages se déplacent en tourbillonnant sous son impulsion, en vue de leur besogne, pour exécuter ses ordres sur la surface du globe terrestre.
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Il les suscite tantôt comme un fléau pour la terre, tantôt comme une source de bienfaits.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Ecoute, Job, tout ceci; lève-toi et considère les merveilles de Dieu.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
Comprends-tu les lois qu’il leur impose et comment il fait briller ses nuages lumineux?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Comprends-tu les déploiements de la nuée, les prodiges de Celui qui possède la science parfaite?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
Toi, dont les vêtements deviennent trop chauds, dès que la terre recouvre le calme sous l’influence du midi,
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
pourrais-tu lui aider à étendre les cieux, solides comme un miroir de métal?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Apprends-moi ce que nous pourrions lui dire: dans les ténèbres où nous sommes, nous manquons d’arguments.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Devra-t-on lui rendre compte quand je parle? Jamais homme a-t-il demandé à être anéanti?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Or donc, personne ne peut regarder le soleil qui brille radieux dans le ciel, lorsque le vent qui passe l’a nettoyé.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Si l’or vient du septentrion, Dieu, lui, demeure couvert d’une redoutable majesté.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
Le Tout-Puissant, nous ne pouvons l’atteindre, lui qui est grand par la force; mais le droit et la parfaite justice, il ne les écrase point!
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
C’Est pourquoi les hommes le révèrent; quant à lui, il n’abaisse ses regards sur aucun des prétendus sages.

< Ayuba 37 >