< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
“My heart pounds [DOU] when [I think about] that.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Listen, all of you, to the thunder, which is like God’s voice [DOU].
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
He causes thunder to be heard all across the sky, and he causes lighting to flash to the most distant places on the earth.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
After [the lightning flashes], we hear the thunder which is like [MET] God’s majestic voice; he does not restrain the lightning when he speaks.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
When God speaks, it is awesome, like thunder; he does amazing things which we cannot [fully] understand.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
He commands the snow to fall on the ground, and [sometimes] he causes it to rain very hard.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
And [when God does that, ] it prevents people [SYN] from working, in order that all people may know that he is the one who has done that (OR, what he can do).
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
[When it rains, ] animals go into their hiding places, and they remain there [until the rain stops].
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
The storms/hurricanes come from the place [in the south where they start], and the cold wind comes from the north.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
[In the (winter/cold season), the cold north wind is like] God’s breath [that] causes [MET] water to freeze; he causes the lakes/streams to become ice.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
God fills the clouds with moisture/hail, and lightning flashes from the clouds.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
He guides the clouds and causes them to move back and forth in order that they may accomplish all that he commands them to do, all over the world.
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Sometimes God sends rain to punish us, and sometimes he sends rain to show us that he acts kindly toward us.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
“Job, listen to this; stop and think about the wonderful things that God does.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
(Do you know how God commands the lightning to flash down from the clouds?/We do not know how God commands the lightning to flash down from the clouds.) [RHQ]
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Only God knows everything perfectly; so (do you know how he causes the clouds to (move/float) (amazingly/wonderfully) across the sky?/you certainly do not know how he causes the clouds to (move/float) (amazingly/wonderfully) across the sky!) [RHQ]
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
No, you just sweat there in your clothes; [it is very oppressive] when the [hot] wind stops blowing from the south and [all the leaves on the trees] (become still/do not move).
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
(Can you stretch out the skies like God does and make them as hard as [SIM] a sheet of polished brass?/You certainly cannot stretch out the skies like God does and make them as hard as [SIM] a sheet of polished brass!) [RHQ]
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
“Job, tell us(exc) what we should say to God; we do not know anything [IDM]. As a result, we do not know what to say to him to defend ourselves.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Should I tell God that I want to speak to him? No, because [if I did that, ] he might destroy me.
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Now, people cannot look [directly] at the sun when it shines brightly in the sky after the wind has blown the clouds away; [so, we certainly cannot look at the brightness of God].
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
God comes out of the north with a light [that shines like] gold; his glory causes us to be afraid.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
Almighty God is very powerful, and we cannot come near to him. He always acts righteously, and he will never oppress us.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
That is the reason that we have an awesome respect for him; he does not pay attention to those who proudly, [but wrongly], think that they are wise.”

< Ayuba 37 >